Zanga Zanga: Jigon APC Ya Fadi Abin da 'Yan Najeriya Ya Kamata Su Yi Wa Tinubu

Zanga Zanga: Jigon APC Ya Fadi Abin da 'Yan Najeriya Ya Kamata Su Yi Wa Tinubu

  • Ƴan Najeriya sun samu shawara daga wajen babban jigo a jam'iyyar APC kan zanga-zangar da ake shirin gudanarwa a faɗin ƙasar
  • Uche Nwosu ya buƙaci matasan Najeriya da su haƙura da zanga-zangar sannan su ba Shugaba Bola Tinubu lokaci ya gyara ƙasar nan
  • Ya bayyana cewa shekara ɗaya da Tinubu ya yi a kan mulki, ta yi kaɗan ya gyara ɓarnar da aka kwashe shekaru ana yi a ƙasar nan

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Jigon jam'iyyar APC, Uche Nwosu, ya roƙi ƴan Najeriya da su ba Shugaba Bola Tinubu lokaci tare da fasa yin zanga-zangar da aka shirya gudanarwa a faɗin ƙasar nan.

Uche Nwosu ya bayyana cewa babu adalci ko kaɗan a yi tsammanin cewa gwamnatin da ta yi shekara ɗaya a kan mulki za ta gyara ɓarnar da aka kwashe shekaru ana yi a ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Zanga zangar adawa da Tinubu: Jam'iyyar APC ta dauki muhimmin mataki

Jigon APC ya ba 'yan Najeriya hakuri kan zanga-zanga
Jigon APC ya bukaci 'yan Najeriya su fasa yin zanga-zanga Hoto: @DOlusegun
Asali: Facebook

"A yi wa Tinubu uzuri" - Jigon APC

Tsohon shugaban ma'aikatan na tsohon gwamnan jihar Imo, Rochas Okorocha, ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa a Abuja ranar Alhamis, cewar jaridar PM News.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jigon na jam'iyyar APC ya nuna cewa ya kamata a yi wa Shugaba Tinubu uzuri, a ba shi lokaci ya gyara ɓarnar da aka yi a ƙasar nan.

Ya bayyana cewa tabbas wasu tsare-tsaren gwamnatin Tinubu sun yi tsauri a yanzu, amma za a ci moriyarsu a nan gaba, rahoton jaridar The Punch ya tabbatar.

Wane kira ya yi kan zanga-zanga?

"Ina amfani da wannan damar domin kira ga matasanmu da su rungumi zaman lafiya. Tabbas muna cikin lokaci mai wuya a matsayinmu na ƙasa. Amma kada mu zama waɗanda gwiwoyinsu suka sare."
"Tabbas a dimokuraɗiyya ƴan ƙasa na da ƴancin yin zanga-zanga amma mafi yawan zanga-zangar da ake yi a Najeriya inda muke da sama da ƙaɓila 250, ba a gama su lafiya."

Kara karanta wannan

Gwamnatin Tinubu ta fadi hanyar magance zanga zangar da ake shirin yi

"Misali a lokacin zanga-zangar lumana ta EndSARS wasu ɓaragurbi sun yi kutse cikinta inda aka lalata kadarori na miliyoyin Naira tare da asarar rayuka masu yawa."

- Uche Nwosu

Karanta wasu labaran kan zanga-zanga

Gwamnatin Tinubu ta bayyana dalilin da ya sa ba ta son a yi zanga-zanga

Ana harin zanga-zanga, Sufeto Janar na ƴan sanda ya aika da saƙo mai zafi

Gwamnonin jihohi 36 sun yi magana kan zanga zangar da matasa ke shirin yi

Babu batun zanga-zanga a Bauchi

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnatin jihar Bauchi ta bayyana cewa ba za a yi zanga-zanga a jihar ta yankin Arewa maso Gabas din ba.

Gwamnatin jihar ta kuma gargaɗi masu shirin gudanar da zanga-zangar da su shiga taitayinsu sannan su sake tunani domin ba za ta lamunci hakan ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng