Shugaba Tinubu Ya Aike da Muhimmin Saƙo Ga Matasa Masu Shirin Yin Zanga Zanga

Shugaba Tinubu Ya Aike da Muhimmin Saƙo Ga Matasa Masu Shirin Yin Zanga Zanga

  • Bola Ahmed Tinubu ya roƙi matasa su yayyafawa zuciyoyin su ruwan sanyi su janye shirinsu na yin zanga-zanga a wata mai kamawa
  • Shugaban ƙasar ya buƙaci su kara masa lokaci domin magance dukkan abubuwan da suka dame su a ƙasar nan
  • Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama'a, Mohammed Idris ne ya bayyana haka a fadar shugaban kasa bayan ganawa da Tinubu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya roƙi matasan ƴan Najeriya su hakura su janye shirinsu na yin zanga-zanga kan ƙuncin rayuwa a wata mai zuwa.

Shugaban ya kuma tabbatarwa da wadanda suka shirya zanga-zangar cewa ya ji kokensu kuma yana bakin kokarinsa wajen ganin an magance duk wata damuwa da ta zame masu alaƙaƙai.

Kara karanta wannan

APC ta fallasa masu shirya zanga zangar adawa da gwamnatin Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu.
Bola Tinubu ya roki matasa su kara masa lokaci, su janye zanga zanga Hoto: Ajuri Ngelale
Asali: Facebook

Ministan yaɗa labarai Mohammed Idris ne ya bayyana haka yayin hira da wasu ƴan jarida jim kaɗan bayan ganawa da Tinubu a Villa yau Talata, Channels tv ta rahoto.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya tura saƙo ga ƴan Najeriya?

Ya ce Shugaba Tinubu ya roƙi masu shirya wannan zanga-zanga mai taken, "kawo karshen gurbataccen shugabanci," su yi haƙuri su janye kudirinsu.

"Batun zanga-zangar da ake shirin yi, shugaban ƙasa ya ce babu bukatar yin hakan, ya roƙi (matasa) su yi hakuri su janye shirinsu, su dakaci matakin da gwamnatin za ta ɗauka kan damuwarsu."
"Ya kamata matasa su saurari shugaban ƙasa, su ƙara ba shi lokaci domin ganin tarin abubuwan alherin da ya shirya masu."

- Mohammed Idris.

Wasu matakai Tinubu ya fara ɗauka?

Dangane da matakan da Tinubu ke ɗauka domin yaye wa ƴan Najeriya kuncin rayuwa, ministan ya ce tuni gwamnatin tarayya ta baiwa jihohi hatsi da buhunan shinkafa.

Kara karanta wannan

Ana harin fara zanga zanga, Sufeto Janar na 'Yan Sanda ya aika da sako mai zafi

Ya ce gwamnatin tarayya za ta ci gaba da tura kayan tallafi zuwa jihohi domin a rabawa ƴan Najeriya da nufin magance yunwa da kuncin rayuwar da ake ciki, Daily Trust ta ruwaito.

IGP ya gargaɗi masu shirin zanga-zanga

A wani rahoton kuma Sufeto-Janar na ƴan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya yi gargaɗi kan zanga-zangar da ake shirin gudanarwa a ƙasar nan.

Kayode Egbetokun ya yi gargaɗin cewa ƴan sanda ba za su zura ido ba su bari a fake da zanga-zangar domin tayar da rikici.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262