Bayan Farmakar Ɗan Majalisar NNPP, An Kama Wani da Ake Zargi da Babban Laifi a Kano

Bayan Farmakar Ɗan Majalisar NNPP, An Kama Wani da Ake Zargi da Babban Laifi a Kano

  • Jami'an tsaro sun kama wani hatsabin mai garkuwa da mutane a yankin ƙaramar hukumar Dawakin Kudu a jihar Kano
  • Rahotanni sun bayyana cewa ana zargin mutumin da sace mutane, bayan haka ya kashe su kana ya ɓinne su a cikin gidansa
  • Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce a halin yanzu suna ci gaba da bincike kan lamarin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Rundunar ƴan sanda reshen jihar Kano ta tabbatar da damƙe ƙasurgumin mai garkuwa da mutane wanda aka gano gawarwaki a gidansa.

Bayanai sun nuna ana zargin mutumin da sace mutane, kashe su da kuma binne su a cikin gidansa da ke ƙaramar hukumar Dawakin Kudu.

Kara karanta wannan

Dubu ta cika: An kama wanda ake zargi da 'kitsa' kisan janar na sojoji a Kano

Taswirar jihar Kano.
Yan sanda sun cafke gawurtaccen mai garkuwa da mutane a Kano
Asali: Original

'Yan sandan Kano sun kama almajiri

A cewar wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta, wanda ake zargin Almajiri ne da ya zo karatu yankin daga baya ya shiga harkar garkuwa da mutane, Tribune Nigeria ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An bayyana cewa wanda ake zargin ya yi garkuwa da wasu mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, wadanda jami’an tsaro suka gano gawarwakinsu a gidansa da ke Dawakin Kudu.

Kano: Wani mataki ƴan sanda suka ɗauka?

Da aka tuntubi jami'in hulɗa da jama'a na rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da kama wanda ake zargin.

Abdullahi Kiyawa ya bayyana cewa a halin yanzu jami'an ƴan sanda sun fara gudanar da bincike kan lamarin domin gano duka masu hannu a wannan ɗanyen aiki.

A cewarsa, rundunar ƴan sanda ta kama wasu da ake zargi da hannu a lamarin bayan tono gawarwaki a gidan mutamin.

Kara karanta wannan

Karshen alewa: Yan sanda sun dakume kwararren barawo ya na tsakiyar sata a Kaduna

Kakakin ƴan sandan ya ce duk da an kama wasu mutane kan lamarin, ƴan sanda na ci gaba da zurfafa bincike.

Yan bindiga sun kashe basarake a Taraba

A wani rahoton na daban, an ji yan bindiga sun kai farmaki kan titin Takum zuwa Chanchangi, sun halaka basarake da ɗansa a jihar Taraba

Gwamna Agbu Kefas ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da kakakinsa ya fitar, ya miƙa sakon ta'aziyya ga iyalansa.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262