“Ba Domin Cin Mutunci Ba Ne”: Gwamna Ya Fadi Dalilin Gyara a Dokar Masarautu

“Ba Domin Cin Mutunci Ba Ne”: Gwamna Ya Fadi Dalilin Gyara a Dokar Masarautu

  • Yayin da ake ta yada jita-jita kan sabuwar dokar masarautu, gwamnatin jihar Oyo ta yi karin haske kan abin da ake yadawa
  • Gwamnatin ta ce dokar da Majalisar ta tabbatar wanda Gwamna Seyi Makinde ya sanyawa hannu ba ta da alaka da hana gadon kujerar
  • Kwamishinan yada labarai a jihar, Dotun Oyelade ya bayyana damuwa kan yadda ake yada abin da kwata-kwata ba a fahimta ba

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Oyo - Gwamnatin jihar Oyo ta yi karin haske kan gyaran fuska game da masarautun jihar da ake ta zarge-zarge a kansu.

Gwamnatin jihar ta musanta zargin da ake yadawa cewa ta dauki matakin ne domin hana gadon kujerar Olubadan.

Kara karanta wannan

An shiga fargaba bayan kazamin hari kan dan takarar gwamna a APC, an rasa rai

Gwamna ya yi karin haske kan gyaran fuska a dokar masarautu
Gwamna Seyi Makinde ya fayyace musabbabin gyaran fuska a dokar masarautu. Hoto: Seyi Makinde.
Asali: Twitter

Masarautu: Gwamna ya fayyace sabuwar doka

An yi yada jita-jitar a lokacin bikin nadin sarautar sabon sarkin Ibadan da ake kira Olubadan, Oba Owolabi Olakulehin, cewar Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An yi bikin madin sarautar a ranar 12 ga watan Yulin 2024 inda aka raba litattafai dauke da sabuwar dokar yayin bikin, Premium Times ta tattaro.

Sabuwar dokar ta samu sahalewar Majalisar jihar Oyo wanda Gwamna Seyi Makinde ya sanyawa hannu.

Gwamnatin Oyo ta soki masu yada jita-jita

Kwamishinan yada labaran jihar, Dotun Oyelade ya ce akwai rashin adalci tsantsa kan abubuwan da mutane suke yadawa.

Oyelade ya ce rashin adalci ne a fara batun sabon sarki mai zuwa a gaba wanda a yanzu ne aka nada Olubadan bai yi ma ko mako daya ba.

Ya ce wasu tun yanzu har sun fara neman ganin karshen sabon Olubadan wanda ko mako daya bai yi ba.

Kara karanta wannan

Gwamnati ta fadi dalilin rokon mazauna Yobe su kauracewa zanga zanga

An nada Olubadan na 43 a Oyo

Kun ji cewa bayan amincewar Gwamna Seyi Makinde a makonnin baya, a ranar Jumu'a 12 ga watan Yuli, 2024 za a nada sabon Olubadan.

Sabon sarkin, Oba Owolabi Akinloye Olakulehin ya kafa tarihin zama Olubadan na 43 wanda ya ke da shekara 85 ya zama sabon sarkin ƙasar Ibadan.

Bayanai sun nuna cewa jim kaɗan bayan kammala naɗa masa rawanin sarautar, Oba Olakuleyin ya koma fadar Ile Osemeji da ke unguwar Oja Oba a birnin Ibadan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.