Duk da Dokar Hana Fita, ’Yan Bindiga Sun Kutsa Kauye da Dare, Sun Hallaka Jama’a

Duk da Dokar Hana Fita, ’Yan Bindiga Sun Kutsa Kauye da Dare, Sun Hallaka Jama’a

  • 'Yan bindiga sun bijirewa dokar hana fita a jihar Benue inda suka kutsa cikin kauye tare da hallaka mutane 18 yayin harin
  • Maharan sun kutsa kauyen Mbacher da ke karamar hukumar Katsina-Ala da misalon karfe 11.00 na daren jiya Juma'a
  • Shugaban karamar hukumar, Justine Shaku shi ya tabbatar da harin inda ya ce sojoji sun kawo dauki amma sun yi latti

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Benue - Wasu 'yan bindiga sun shammaci mazauna wani kauye da tsakar dare inda suka hallaka mutane 18 a jihar Benue.

Lamarin ya faru ne da karfe 11.00 na daren jiya Juma'a 19 ga watan Yulin 2024 a kauyen Mbacher da ke karamar hukumar Katsina-Ala.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun bindige shugaban Miyetti Allah, kungiyar makiyaya ta yi kira ga mutanenta

'Yan bindiga sun yi sanadin mutuwar mutane 18 a jihar Benue
'Yan bindiga sun shammaci 'yan kauye inda suka hallaka 18 a jihar Benue. Hoto: Legit.
Asali: Original

Benue: 'Yan bindiga sun tafka barna

Harin na zuwa ne bayan gwamnatin jihar ta sanya dokar hana fita daga shida na yamma zuwa safiya, cewar Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Maharan sun yi fatali da dokar inda suka fito tare da hallaka mazauna yankunan da dama tare da tafka barna.

Maharan sun jera mutanen kamar za su yi musu jawabi amma daga bisani sai suka bude musu wuta, Tribune ta tattaro.

Benue: Shugaban karamar hukuma ya magantu

Shugaban karamar hukumar Katsina-Ala, Justine Shaku ya yi Allah wadai da harin inda ya ce maharan sun gama barna kafin zuwan sojoji.

"Da misalin karfe 11.00 na daren jiya Juma'a mun samu labarin cewa mahara sun shigo kauyen inda suke shiga gida-gida suna fito da su."
"Na yi gaggawar samun dakarun sojoji a Tor Doonga sai dai abin takaici kafin isowarsu maharan har sun hallaka mutane sun tsere."

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun je har gida, sun harbe basarake har lahira a Arewa

- Justine Shaku

Shaku ya kara da cewa wasu daga cikin mutane sun gamu da raunuka yayin harin inda ya jajantawa wadanda suka rasa rayukansu.

'Yan bindiga sun sace shugaban Kwaleji

Kun ji cewa ƴan bindiga sun yi garkuwa da mukaddashin shugaban kwalejin fasaha ta jihar Benue, da ke Ugbokolo, Dakta Emmanuel Barki.

Barki da sauran ma'aikata biyu na kwalejin da direbansu, an sace su ne a kan hanyar su ta dawowa zuwa Ugbokolo bayan sun je wani aiki a Makurdi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.