Zanga Zanga Ta Samu Babban Koma Baya, an Saka Sabanin Kabilanci a Cikin Tafiyar

Zanga Zanga Ta Samu Babban Koma Baya, an Saka Sabanin Kabilanci a Cikin Tafiyar

  • Kungiyar yan ƙabilar Ibo ta nuna fargabar kan shirin zanga zanga da ake yi a faɗin Najeriya saboda tsadar rayuwa da ake fuskanta
  • Kungiyar Ọhanaeze Ndigbo ta yi kira na musamman ga yan kabilar Ibo da ke zaune a Arewa kan kaucewa zanga zangar da ake shirin yi a Agusta
  • Ohaneze ta bayyana dalilai kan abin da yasa ta yi kira na musamman ga mutanenta a wannan karon musamman lura da abin da ya faru a baya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Nigeria - Kungiyar yan kabilar Ibo a Najeriya ta dauki matakin da zai kawo koma baya ga shirin zanga zanga da matasa ke yi a Najeriya.

Kara karanta wannan

Tarihi bai manta ba: Nasarori da matsalolin da aka samu lokutan zanga zanga a baya a Najeriya

Kungiyar ta bukaci ƴaƴanta su kauracewa zanga zangar a sassa daban-daban na tarayyar Najeriya.

Zanga zanga
An bukaci yan kabilar Ibo su kauracewa zanga zanga. Hoto: Kola Sulaimon
Asali: Getty Images

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa kungiyar Ọhanaeze Ndigbo ta bayyana dalilai kan maganar da ta yi ga ƴaƴanta.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ohanaeze ta yi kira kan zanga zanga

Kungiyar Ọhanaeze Ndigboe ta kabilar Ibo a Najeriya ta yi kira ga yan kungiyar da ke Arewacin Najeriya kan cewa su nisanci tarayya cikin zanga zangar da ake shirin yi.

Haka zalika kungiyar ta umurci ƴaƴanta a kudu maso yammacin Najeriya su dauki matakin kin fita zanga zanga.

Mazi Okechukwu Isiguzoro ne ya fitar da sanarwar ga ƴaƴanta kungiyar a ranar Talata da ta wuce, rahoton Punch.

Dalilin kiran Ohanaeze kan zanga zanga

Mazi Okechukwu Isiguzoro ya ce sun dauki matakin ne duba da yadda aka samu matsaloli a kan zanga zanga a tarihi.

Kara karanta wannan

Adawa da Tinubu: Gwamnati ta gano wadanda ke daukar nauyin matasa su yi zanga zanga

Jagoran yan kabilar Ibon ya ce a shekarar 1978 an yi zanga zangar 'Ali Must Go' inda aka rika cutar da mutanensu.

Ya kuma kara da cewa an samu wasu zanga zanga da aka yi a baya wanda an cutar da yan kabilar Ibo saboda haka ne suka dauki mataki a wannan karon.

Zanga zanga: AYCF ta shawarci matasa

A wani rahoton, kun ji cewa kungiyar Arewa Youth Consultative Forum (AYCF) ta yi kira na musamman ga matasa da ke shirin fita zanga zanga a Najeriya.

Kungiyar ta ba matasan shawara kan yadda ya kamata zanga zangar ta kasance domin kaucewa barkewar rikici da sace sace a Najeriya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng