Zanga Zanga: Matasan Arewa Sun Yi Gargadi, Sun Fadi Makarkashiyar da Ake Shiryawa

Zanga Zanga: Matasan Arewa Sun Yi Gargadi, Sun Fadi Makarkashiyar da Ake Shiryawa

  • Yayin da ake shirye-shiryen gudanar da zanga-zanga, kungiyar matasa a Arewa ta yi gargadi kan haka
  • Kungiyar mai suna Arewa Youth Federation ta barranta kanta ta zanga-zangar inda ta ce ana ƙoƙarin mayar da Najeriya baya
  • Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban kungiyar, Kabir Mutazu ya fitar inda ya gargadi matasa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Wata kungiyar matasa a Arewacin Najeriya ta bayyana matsayarta kan shirye-shiryen zanga-zanga.

Kungiyar mai suna Arewa Youth Federation (AYF) ta barranta kanta da zanga-zanga kan gwamnatin Bola Tinubu.

Matasa a Arewa sun barranta kansu da zanga-zanga a Najeriya
Kungiyar Arewa Youth Federation ta yi fatali da zanga-zanga da ake shirin yi. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

Zanga-zanga: Kungiyar matasan Arewa ta yi gargadi

Shugaban kungiyar, Kabir Mutazu ya tabbatar da haka inda ya ce duka rassan kungiyar a jihohin Arewa ba za su shiga zanga-zangar ba a cewar Daily Nigerian.

Kara karanta wannan

Kungiyar Arewa ta fatattaki shugabanta saboda goyon bayan shirya zanga zanga

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Matazu ya ce mafi yawan masu zanga-zangar suna da wani nufi na mugunta ga kasar domin kawo tashin hankali, Pulse ta tattaro.

"Kungiyar ƴan Arewa ta fahimci yanayin yadda ƙasar ke ciki kuma masu zanga-zangar sun rasa tsari a shirinsu."
"Gudanar da zanga-zanga a wannan hali zai kara rusa ci gaban da aka samu a kasar wanda aka sha wahala wurin samar da shi."
"Arewa Youth Federation ba ta goyon bayan zanga-zangar inda take tare dari bisa dari da gwamnatin Bola Tinubu domin shawo kan matsalolin yankin."

- Kabir Mutazu

Kungiyar AYF ta shawarci Arewa kan zanga-zanga

Kungiyar ta bukaci ƴan Najeriya da su yi fatali da kiran zanga-zangar inda ta ce akwai makarkashiya a ciki.

Ta ce wasu ne marasa kishin kasa ke neman kawo rigima da tarwatsa ci gaban da aka dade ana nema.

Kara karanta wannan

Ana wata ga wata: APC ta fadi abin da za ta yi domin hana matasa zanga zanga

Kungiyar AYA ta kori shugaba kan zanga-zanga

Kun ji cewa Kungiyar matasan ta Arewa Youth Ambassadors (AYA) to kori shugabanta, Yahaya Abdullahi kan zanga-zanga.

Kungiyar ta ce ta dauki matakin korar tsohon shugaban ne bisa zargin tattaro kawunan matasa domin zanga-zangar.

AYA ta nemi a binciki tsohon shugabanta, Yahaya Abdullahi da laifin cin hanci wurin shirya zanga-zanga.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.