Jos: Ginin Makaranta Ya Rufta Kan Ɗalibai Suna Tsakiyar Zana Jarabawa

Jos: Ginin Makaranta Ya Rufta Kan Ɗalibai Suna Tsakiyar Zana Jarabawa

  • Ginin wata makaranta ya rushe kan ɗalibai da ke tsakiyar rubuta jarabawa a Busa Buji da ke ƙaramar hukumar Jos a jihar Filato
  • Rahotanni sun bayyana cewa iyayen yara sun garzaya wurin suna kukan neman agaji kuma tuni jami'an tsaro suka dura makarantar
  • Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:00 na safiyar yau Jumu'a, 12 ga watan Yuli, 2024, yanzu haka an fara kokarin zakulo ɗaliban da ginin ya danne

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jos, jihar Plateau - Rahotannin da muka samu sun nuna cewa yanzu haka dalibai da yawa sun makale a wata makaranta da ta rufta ana tsakiyar jarabawa a jihar Filato.

Lamarin ya faru ne a wata makaranta da ke unguwar Busa Buji a ƙaramar hukumar Jos ta jihar Filato a shiyyar Arewa ta Tsakiya.

Kara karanta wannan

Jami'an DSS sun kai samame gidan wani da ake zargi da alaƙa da ƴan bindiga

Taswirar jihar Plateau.
Makaranta ta rufka kan ɗalibai ana tsakiyar zana jarabawa a Jos
Asali: Original

A cewar shaidun gani da ido, ginin makarantar Saint Academy ya fado ne da misalin karfe 11 na safiyar yau Juma’a, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ganau sun bayyana cewa ginin ya danne ɗalibai da dama waɗanda ke zana jarabawa a makarantar.

An tattaro cewa bayan labarin rushewar ginin makarantar ya bazu a yankin, iyayen yara sun garzaya makaranta cikin tashin hankali suna kuka neman a ceto ƴaƴansu.

Jami'an tsaro sun kai ɗauki

Legit Hausa ta fahimci cewa yanzu haka an fara aikin ceto ɗaliban kuma jami'an tsaro da suka haɗa da sojoji da ƴan sanda sun isa wurin.

Haka nan kuma wata babbar mota da ta nufi wurin da ibtila'in ya afku domin kai agaji ta maƙale a taɓo sakamakon ruwan saman da aka yi.

Jos: Ana fargabar ɗalibai sun mutu

Kara karanta wannan

Plateau: An kashe mataimakin kwamandan rundunar sojojin Najeriya

Wasu rahotanni sun yi ikirarin cewa an rasa rayuka sakamakon kifewar ginin makarantar amma a halin yanzu bamu da tabbacin faruwar hakan.

Kawo yanzu an yi nasarar ceto ɗaliban da ginin ya danne kuma tuni aka ɗauke su zuwa asibiti domin kula da lafiyarsu, rahoton Premium Times.

Babban limamin Jos ya rasu

A wani rahoton kun ji cewa Babban limamin masallacin Juma'a da ke birnin Jos a jihar Plateau, Sheikh Lawal Adam Abubakar ya rasu.

Marigayin ya riga mu gidan gaskiya ne a ranar Alhamis da ta gabata 11 ga watan Yulin 2024 a asibitin Jos yana da shekaru 80 a duniya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262