Ana Murnar Janye Haraji, Gwamnati ta Gindaya Sharadi Kan Farashin Kaya

Ana Murnar Janye Haraji, Gwamnati ta Gindaya Sharadi Kan Farashin Kaya

  • Gwamnatin tarayya ta ce za ta kayyade farashin abincin da za a rika shigowa da shi kasar nan idan an janye haraji
  • Ministan noma da samar da abinci, Abubakar Kyari ne ya bayyana haka inda yace gwamnati za ta dauki matakin kawar da yunwa
  • Ministan ya ce gwamnati za ta dauki matakan kawar da yunwa domin tabbatar da cewa yan kasa sun samu sauki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa. Abuja- Yayin da ake murna kan janye haraji kan wasu nau'in abinci, gwamnatin tarayya ta ce akwai sharadi kan farashin abinci. Matakin na zuwa bayan gwamnatin ta bayyana cewa za a janye harajin shinkafa, masara da alkama da wasu nau'in abinci.

Kara karanta wannan

"Sai an bi a hankali": 'Yan kasuwa sun yi murna da janye harajin shigo da abinci

Abinci
Gwamnati za ta kayyade farashin abinci
Asali: Getty Images

A sakon da ya wallafa a shafinsa na X, Ministan noma da samar da abinci, Abubakar Kyari ya ce gwamnati za ta tabbatar da karya farashin abinci.

"Za a magance yunwa": Minista

Ministan noma da samar da abinci, Abubakar Kyari ya bayyana cewa ana daukar matakin kawar da yunwa a Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jaridar Vanguard ta wallafa cewa Ministan ya ce za a dauki matakin tabbatar da cewa an kayyade farashin abincin da za a shigo da shi.

Ya ce tunda gwamnati ta amince da janye harajin wasu nau'in abinci na kwanaki, za a sanya idanu wajen tabbatar da farashin da za a sayar da abincin a kasuwanni.

Ministan ya nanata cewa gwamnati za ta shigo da tan 250,000 na masara da alkama, a yunkurin tabbatar da cewa an daina kwana da yunwa a kasar nan.

Kara karanta wannan

Bayan matakin bude iyakokin kasa, gwamnati ta fadi lokacin ragargajewar farashin abinci

Daga sauran matakan da ya ce za a dauka akwai tallafawa kananan manoma wajen noman damuna da na rani.

"Farashin abinci ba zai sauko ba:" Yan kasuwa

A baya kun ji cewa kungiyar yan kasuwa ta bayyana cewa dakatar da harajin abincin ba zai kawo saukin farashi ba. Shugaban kungiyar 'yan kasuwa a Kano, Dr. AbdulAziz Bature ya ce akwai hanyoyin da ya kamata a bi wajen kawar da yunwa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano.