'Yan Bindiga Sun Kai Hari da Tsakar Dare, Sun Hallaka Bayin Allah da Dama

'Yan Bindiga Sun Kai Hari da Tsakar Dare, Sun Hallaka Bayin Allah da Dama

  • Ƴan bindiga sun aikata ta'adi yayin da suka kai farmaki kauyen Ama Hausa da ke ƙaramar hukumar Okigwe a jihar Imo
  • Bayanai sun nuna cewa maharan sun kashe mutum shida a harin wanda ya shafe tsawon sa'o'i gabanin sojoji su kai ɗauki
  • Kwamishinan ƴan sandan jihar Imo, CP Ɗanjuma ya ce dakarun ƴan sanda ba za su huta ba sai sun tabbata sun cafke dukkan masu hannu a kisan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Imo - Ƴan bindiga sun kashe mutane shida a wani hari da suka kai kauyen Ama Hausa da ke karamar hukumar Okigwe a jihar Imo, kudu maso gabashin Najeriya.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun far wa al'ummar kauyen ba zato ba tsammani da tsakar daren ranar Laraba da ta gabata.

Kara karanta wannan

Zamfara: 'Yan bindiga 100 sun kai hari kan bayin Allah, sun tafka mummunar ɓarna

Yan sandan Najeriya.
Yan bindiga sun kashe mutane 6 a jihar Imo Hoto: Nigeria Police Force
Asali: Twitter

Lamarin ya faru ne sa'o'i kadan kafin wani hari na daban da aka kai ofishin 'yan sanda a karamar hukumar Ivo a jihar Ebonyi, kamar yadda Premium Times ta kawo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kamar dai a Ebonyi, ana zargin ‘yan bindigar da suka kai hari a jihar Imo ’yan kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra ne (IPOB) da mayaƙansu ESN.

A yayin harin da aka kai yankin ƙaramar hukumr Okigwe, maharan sun ci karensu babu babbaka har zuwa karfe 9 na safiyar ranar Alhamis.

Wane mataki jami'an tsaro suka ɗauka?

A rahoton da jaridar Punch ta wallafa, sai bayan wayewar gari sannan jami'an rundunar sojojin Najeriya suka isa garin domin kai ɗauki.

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar Imo, Aboki Danjuma, ya sha alwashin cewa ‘yan sandan jihar za su zakulo wadanda suka yi kisan.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai mummunan hari ofishin ƴan sandan Ebonyi, an kashe mutane 5

CP Danjuma ya faɗi hakan ne a lokacin da ya kai ziyara wurin da aka kai harin ranar Alhamis. 

'Ina mai tabbatar muku da cewa rundunar ƴan sanda ba za ta yi ƙasa a guiwa har sai an kama wadanda suka aikata wannan aika-aika kuma an gurfanar da su a gaban kotu,” in ji shi.

Kwamishinan ya ce a halin yanzu ‘yan sanda tare da hadin gwiwar sojoji da ’yan banga sun bazama domin kakkabe ‘yan bindigar da ke da alhakin kisan.

Yan sanda sun mutu a harin Abia

Kuna da labarin Ƴan bindiga sun kai hari shingen binciken ababen hawa, sun kashe ƴan sanda biyu tare da jikkata wani a Aba da ke jihar Abia.

Lamarin dai ya tayar da hankulan mutanen da ke yankin waɗanda suka kulle shaguna suka koma gida gabanin a ƙara girke ƴan sanda a wurin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel