Kano: Adadin Mutanen da Suka Mutu Sakamakon Harin da Aka Kai Masallaci Ya Ƙaru

Kano: Adadin Mutanen da Suka Mutu Sakamakon Harin da Aka Kai Masallaci Ya Ƙaru

  • Adadin Musulman da suka rasu sakamakon harin masallacin da wani mutumi ya kai a jihar Kano ya ƙaru zuwa 23
  • Bincike ya nuna cewa mutum 22 daga cikin 24 da aka kwantar a asibitin Murtala Muhammad sun rasu, wani mutum ɗaya ya rasu asibitin Aminu Kano
  • Shafiu Abubakar, ɗan shekara 38 ne ya bankawa masallacin wuta a lokacin da Musulmai ke tsaka da Sallar asuba a Larabar Abasawa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - An samu ƙarin mutanen da suka rasu sakamakon harin da wani matashi ya kai Masallaci a Larabar Abasawa, karamar hukumar Gezawa a Kano.

Shafi’u Abubakar, ɗan kimanin shekaru 38 ne ya bankawa Masallacin wuta yayin da mutane ke tsaka da Sallar Asubah a watan Mayun da ya gabata.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun yi yunƙurin takaita babban limamin Musulmi a jihar Kaduna

Taswirar Kano.
Mutanen da suka rasu sakamakon harin Masallaci a jihar Kano sun kai 23
Asali: Original

A wani bincike, jaridar Daily Trust ta gano cewa adadin waɗanda suka rasu sakamakon ibtila'in sun ƙaru zuwa 23.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mutum 23 sun rasu a harin masallacin Kano

Binciken da aka yi a asibitin Murtala Muhammad, inda aka kwantar da waɗanda suka jikkata, ya nuna cewa 22 daga cikin mutum 24 sun mutu.

Mutum daya da aka kai Asibitin Koyarwa na Aminu Kano shi ma ya mutu sakamakon raunuka da ya ji, hakan ya sa adadin wadanda suka mutu ya zama 23.

Akwai wanda ya kwance a AKTH Kano

An tattaro cewa har yanzun akwai ragowar mutum ɗaya da ke kwance a asibiti yana jinya, an sallami ɗaya ya koma gida, sai kuma mutum biyu da suka tsira daga harin.

Ana zargin Shafiu Abubakar ya yi amfani da fetur, ya wanke masallacin tare da kulle ƙofofi, sannan ya cinnawa masallata akalla 30 wuta suna cikin Sallar asuba.

Kara karanta wannan

Yobe: Wata matar aure ta soka wa mijinta wuƙa har lahira, ta yi bayanin abin da ya faru

Bayan aikata wannan ɗanyen aiki, wanda ake zargin ya shaidawa ƴan sanda cewa ya yi haka ne domin hukunta waɗanda yake zargin sun zalunce shi a rabon gadon gidansu.

Kano: An gurfanar da Shafi'u gaban kotu

Tuni dai aka gurfanar da wanda ake zargin a gaban wata kotun shari’ar Musulunci karkashin jagorancin Mai Shari'a Halhalatu Zakariyya.

Bayan haka ne kotun ta bayar da umarnin a tsare shi a gidan gyaran hali kafin zama na gaba.

Ƴan bindiga sun sace shanun Liman

A wani rahoton kuma Ƴan bindiga sun kai hari kauyen Gidan-Makera a ƙaramar hukumar Kagarko da ke jihar Kaduna, sun tafi da shanun babban limamin garin.

Mazauna yankin sun bayyana cewa wasu ƴan banga sun yi nasarar kwato shanun bayan sun bi bayansu ranar Talata.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel