Bidiyo: Muhammadu Sanusi II Ya Gana da Fitaccen Malamin Musulunci a Fadar Sarkin Kano

Bidiyo: Muhammadu Sanusi II Ya Gana da Fitaccen Malamin Musulunci a Fadar Sarkin Kano

  • Muhammadu Sanusi II ya ƙarbi bakuncin babban malamin addinin musulunci daga Maiduguri, jihar Borno, Sheikh Ali Abulfatahi
  • Sheikh Abdulfatahi tare da tawagarsa sun kai wa Sanusi ziyara fadar Sarkin Kano ranar Litinin, 24 ga watan Yuni, 2024
  • Wannan na zuwa ne a lokacin da ake ci gaba da taƙaddama kan sarautar Kano tun bayan rusa masarautu biyar da Abdullahi Ganduje ya kirƙiro

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Babban malamin addinin Musulunci a Maiduguri, jihar Borno, Khalifa Sheikh Ali Abulfatahi ya ziyarci mai martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II.

Sarkin ya karɓi bakuncin fitaccen malamin da ƴan tawagarsa a fadarsa da ke Ƙofar Kudu a cikin kwaryar birnin Kano.

Kara karanta wannan

Tinubu ya sake ɗauko tsohon kwamishinansa, ya naɗa shi a shirgegen muƙami

Muhammadu Sanusi II.
Babban malami daga Maiduguri ya ziyarci Muhammadu Sanusi II a Kano Hoto: Masarautar Kano
Asali: Twitter

Hakan na ƙunshe ne a wani saƙo da masarautar Kano ta wallafa a shafinta na manhajar X wanda aka fi sani da Twitter ranar Litinin, 24 ga watan Yuni, 2024.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammad Sanusi ll CON, ya karbi bakuncin Khalifa Sheikh Ali Abulfatahi daga Maiduguri."

Yadda aka fara rigimar sarautar Kano

Wannan ziyara na zuwa ne a daidai loƙacin da rigimar sarautar Kano ke ƙara ƙamari tsakanin Sanusi II da sarki na 15, Aminu Ado Bayero.

Idan ba ku manta ba Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dawo da Sanusi II kan kujerar Sarkin Kano a watan Mayun 2024.

Sai dai wannan mataki bai yiwa Aminu Ado daɗi ba, wanda har yanzu yake zaune a ƙaramar fadar Nassarawa da ke cikin birnin Kano.

A makon jiya, babbar kotun tarayya mai zama a Kano rusa matakin dawo da Muhammadu Sanusi saboda Gwamna Abba ya take umarnin alƙali.

Kara karanta wannan

Ana tsaka da rikicin sarauta, Ganduje ya yi babban rashi a jihar Kano

Hukuncin kotun ya bar baya da ƙura yayin da Gwamnatin Kano ta fito ta jaddada cewa Muhammadu Sanusi II na nan daram, ba wanda ya tsige shi.

Yan sanda sun girke jami'an tsaro

A wani rahoton kuma rundunar ƴan sanda ta bayyana dalilin da ya sa ta turan ƙarin jami’anta zuwa fadar da Muhammmadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero.

Kwamishinan ƴan sandan jihar mai barin gado, AIG Usaini Gumel, ya bayyana cewa an tura ƙarin jami'an tsaron ne domin samar da tsaro a wuraren guda biyu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262