'Yan Sanda Sun Yi Magana Yayin da Kotu Ke Shirin Sanar da Halataccen Sarkin Kano

'Yan Sanda Sun Yi Magana Yayin da Kotu Ke Shirin Sanar da Halataccen Sarkin Kano

  • Yayin da ake dakon hukuncin Babbar Kotun Tarayya kan rikicin sarauta, rundunar ƴan sanda ta buƙaci al'ummar jihar Kano su zauna lafiya
  • Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar, SP Abdullahi Kiyawa ya ce za a tura ƙarin jami'an tsaro domin tabbatar da doka da oda
  • A yau Alhamis, 20 ga watan Yuni, 2024 kotun za ta yanke hukunci kan sahihancin dokar rusa masarautu da mayar da Sanusi II

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Rundunar ƴan sanda reshen jihar Kano ta roƙi jama'a su zauna lafiya a lokacin da ake dakon hukuncin Babban Kotun Tarayya kan rigimar sarauta.

Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da jami'in hulda da jama'a na rundunar ƴan sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa ya fitar a Kano ranar Alhamis.

Kara karanta wannan

Kotu ta yi magana yayin da ake jiran yanke Hukunci kan sahihancin tuɓe Sarkin Kano

CP Usaini Gumel
Yan sanda sun roki jama'a su zauna lafiya yayin da kotu za ta yi hukunci yau Hoto: Kano Police Command
Asali: Facebook

Kamar yadda Vanguard ta ruwaito, Abdullahi Kiyawa ya nanata kudurin hukumar na kare rayuka da dukiyoyin al'umma.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kakakin ƴan sandan ya kuma gargadi duk wani mai yunkurin tayar da zaune tsaye bayan hukuncin kotu ya gaggauta canza tunani.

Kano: Wani mataki ƴan sanda suka ɗauka?

"Tare da haɗin guiwar sauran hukumomin tsaro, rundunar ƴan sanda za ta tabbatar da dokar haramta zanga-zanga da wasu tarurruka da gwamnatin Kano ta yi."
"Duk wanda ya yi kunnen ƙashi zai ɗanɗana kuɗarsa domin za a girke ƙarin dakarun tsaro da za su tabbatar da bin doka da oda.
"Muna kira ga al'umma su ba jami'an tsaro haɗin kai kuma su taimaka mana da sahihan bayanai don mu gudanar da aikinmu na tabbatar da zaman lafiya."

- Abdullahi Kiyawa.

Rundunar ƴan sandan ta kuma shawarci sauran jami'an tsaron da ba na gwamnati ba kamar ƴan banga da mafarauta su guji shiga harkokin tsaro.

Kara karanta wannan

Fargaba yayin da Kotun Tarayya za ta yanke hukunci kan halaccin tsige Sarkin Kano

Wannan dai na zuwa ne yayin da Babbar Kotun Tarayya ke shirin yanke hukunci kan sahihancin dokar rushe masarautun Kano da dawo da Muhammadu Sanusi II, rahoton Leadership.

Ɗan Kwankwasiyya ya faɗi halin da suke ciki

Wani ɗan Kwankwasiyya, Sanusi Isiyaku ya shaidawa Legit Hausa cewa babu abin da ke faruwa na tashin hankali a Kano kan batun sarauta.

Sanusi ya ce kowa na ci gaba da harkokinsa kamar kullum bayan wayewar gari, wasu ma ba su san yau za a yanke wani hukunci a kotu ba.

"Lafiya kalau muke zaune, wasu ma ba su san meke faruwa a kotu ba, duk wanda ya tayar da zaune tsaye ɗan can ɓangaren ne kuma su dama haka suke so.
"Muna fatan jami'an tsaro za su ɗauki matakin da ya dace duk da mun ga bangaren da suke goyon baya, Allah ya ci gaba da kare Kano daga masu ƙulla makirci," in ji shi.

Kara karanta wannan

Murna ta koma ciki, 'yan bindiga sun hallaka Amarya mako 1 tak bayan ɗaura aurenta

Majalisar Kano ta ɗaukaka ƙara

A wani rahoton kuma Majalisar dokokin jihar Kano ta garzaya kotun ɗaukaka ƙara kan rigimar sarautar da ta ƙi ci kuma ta ƙi cinyewa a jihar.

Majalisar ta roƙi kotun ɗaukaka ƙara ta dakatar da shari'ar da Sarkin Dawaki Babba, Aminu Babba Danagundi ya shigar gaban babban kotun tarayya.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel