"Ka Yafewa Maƙiya," Matasan Arewa Sun Aike da Sako Ga Sarki Aminu Ado Bayero

"Ka Yafewa Maƙiya," Matasan Arewa Sun Aike da Sako Ga Sarki Aminu Ado Bayero

  • Matasan Arewa sun tura sakon barka da Sallah da nuna goyon baya ga Mai Martaba Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero
  • A wata sanarwa da shugaban ƙungiyar matasan Arewa (AYAF), Nuhu Magaji ya fitar, ya roƙi basaraken ya yafe wa maƙiyansa
  • Ya kuma yi kira ga ɗaukacin mazauna Kano da su rungumi zaman lafiya da ƙaunar juna domin kawo ci gaba mai ɗorewa a jihar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano - Ƙungiyar matasan Arewa (AYAF) ta aike saƙon barka da Sallah ga Sarki na 15, Aminu Ado Bayero a jihar Kano.

Matasan sun roƙi basaraken da ya ci gaba da jagorantar al'ummar jihar Kano ba tare da nuna gajiyawa ba kuma ya yafewa waɗanda suka nuna masa ƙiyayya.

Kara karanta wannan

Sojojin Najeriya sun hallaka ƴan bindiga sama da 100 ana shagalin Sallah a Arewa

Sarki Aminu Ado Bayero.
Kungiyar matasan Arewa ta yiwa Sarki Aminu Ado Bayero barka da Sallah Hoto: @Imranmuhdz
Asali: Facebook

Shugaban ƙungiyar AYAF, Nuhu Magaji ne ya bayyana hakan a wata sanarwa ta barka da Sallah da ya fitar ranar Lahadi, kamar yadda The Cable ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kuma yabawa Sarkin Kano na 15 bisa jajircewarsa wajen ganin an samu hadin kai tsakanin al'umma da kuma ci gaban Kano.

Matasan Arewa sun goyi bayan Sarki Aminu

"A wannan lokacin da Musulmi ke gudanar da bukukuwan babbar Sallah, kungiyar ci gaban matasa ta Arewa (AYAF) na mika sakon Barka da Sallaj ga Mai Martaba Sarki Aminu Ado Bayero.
"Duk da taƙaddama da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan, muna goyon bayan Sarki Aminu Bayero, wanda ya kasance ginshiƙin zaman lafiya, ci gaba, da kwanciyar hankali.
“Sarkin Aminu ya sadaukar da kansa ga masarauta, kuma abubuwan da ya yi sun zama abin koyi gare mu. Mun fahimci irin namijin kokarin da yake yi na inganta hadin kai, fahimtar juna, da ci gaba a Kano da ƙasa baki ɗaya."

Kara karanta wannan

Babbar Sallah: Sarki Sanusi ya tura sakwanni biyu ga Kanawa a ranar sallah

- Nuhu Magaji.

Kungiyar matasan ta kuma yi kira ga ɗaukacin mazauna Kano da su rungumi zaman lafiya da haɗin kai domin ci gaban jihar, kamar yadda Daily Post ta rahoto.

Kotu za ta raba gardama a shari'ar sarauta

A wani rahoton na daban Babbar Kotun Tarayya mai zama a Kano ta shirya yanke hukunci kan sahihancin mayar da Muhammadu Sanusi II kan sarautar Kano.

Kotun ta zaɓi ranar 20 ga watan Yuni, 2024 domin yanke hukunci kanɓhalascin sabuwar dokar masarautar Kano da Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta yi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel