Karo Na 2: Ramin Hako Ma’adanai Ya Rufta da Mutane a Neja, Jama’a Sun Rasu

Karo Na 2: Ramin Hako Ma’adanai Ya Rufta da Mutane a Neja, Jama’a Sun Rasu

  • Bayan kwanaki an kara samun ruftawar ramin ma'adanai da mutane a jihar Neja da ke Arewa maso tsakiyar Najeriya
  • Rahotanni sun nuna cewa hakan ya faru ne bayan mutane sama da 20 sun mutu a wani ramin a jihar ranar 3 ga watan Yuni
  • Shugaban hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar, Alhaji Abdullahi Baba-Arah ya yi karin haske kan halin da ake ciki

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Jihar Niger - Rahotanni suna kara nuni da cewa an sake samun ruftawar ramin hako ma'adanai a jihar Neja.

Hakan na zuwa ne kwanaki kadan bayan mutane sama da 20 sun mutu a hatsarin ramin ma'adanai garin Galkago da ke jihar.

Kara karanta wannan

Gwamnati ta kirkiro shirin musamman ga matasa masu hidimar NYSC

Niger Map
Rami ya sake ruftawa da mutane a Neja. Hoto: Legit
Asali: Original

Jaridar Leadership ta ruwaito shugaban hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar (NSEMA) yana karin haske kan lamarin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A wane yanki ramin ya rufta?

Rahotanni sun nuna cewa ramin ya rufta ne a kauyen Bazakwoi a yankin Adnun da ke jihar, rahoton jaridar The Guardian.

Har ila yau an ruwaito cewa a jiya Alhamis, 13 ga watan Yuni ne lamarin ya faru yayin da mutane ke tsaka da hakar ma'adinai a ramin.

Shugaban NSEMA ya yi magana

Shugaban hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar (NSEMA) Alhaji Abdullahi Baba-Arah ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai.

Alhaji Abdullahi Baba-Arah ya kara da cewa hatsarin shi ne na biyu cikin kwanaki 10 da suka wuce a jihar.

Mutum nawa suka mutu a Neja?

Har ila yau, shugaban NSEMA na jihar ya tabbata cewa an samu mutane uku da ruftawar ramin ya yi sanadiyyar mutuwarsu.

Kara karanta wannan

Goodluck Jonathan ya bayyana nasara 1 da Najeriya ta samu saboda dimokuraɗiyya

Shugaban ya kuma kara da cewa al'ummar wurin sun yi kokarin ceto mutum daya da bai riga ya mutu ba.

Abdullahi Baba-Arah ya kuma tabbatar da cewa a halin yanzu ba wani mutum da ya makale a cikin ramin.

Rami ya rufta da mutane a Zamfara

A wani rahoton, kun ji cewa rayukan mutum uku sun salwanta bayan wani ramin haƙar ma'adanai ya rufto kan ma'aikata a Zamfara.

Rahotanni sun yi nuni da cewa ramin da ya rufto a ƙaramar hukumar Anka ta jihar ya kuma yi sanadiyyar jikkata rayukan mutum 11.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng

Online view pixel