12 ga Yuni: 'Yar'Adua, Abiola da Mutane 30 da Suka Tabbatar da Dimokuradiyyar Najeriya

12 ga Yuni: 'Yar'Adua, Abiola da Mutane 30 da Suka Tabbatar da Dimokuradiyyar Najeriya

Abuja - Shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya lissafa sunayen wasu 'yan mazan jiya da ya ce su ne suka sadaukar da rayuwarsu domin tabbatar dimokuraɗiyyar ƙasar nan.

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Shugaba Bola Tinubu ya ce shekaru 31 da suka gabata, Najeriya ta tsaya tsayin daka domin ganin cewa ta koma kan turbar mulki na dimokuraɗiyya.

Shugaban kasar ya bayyana hakan ne a jawabin kai tsaye da ya gabatar a ranar Laraba, 12 ga watan Yuni, kamar yadda hadimin Tinubu, Bayo Onanuga ya wallafa a X.

Tinubu ya yi magana kan dimokuradiyyar Najeriya
Tinubu ya zayyana gwarazan dimokuradiyyar Najeriya. Hoto: @aonanuga1956
Asali: Twitter

A jawabin zagayowar ranar dimokuraɗiyyar Najeriya na shekarar 2024, Tinubu ya lissafa wadanda suka tabbatar da dimokuraɗiyyar ƙasar na shekaru 25.

Kara karanta wannan

Bola Tinubu ya ɗauki matsaya, zai miƙa sabon mafi ƙarancin albashi ga majalisa

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya lissafo gwarazan dimokuraɗiyya

Ga jerin akalla mutane 32 da Shugaba Tinubu ya ayyana a matsayin gwarazan dimokuraɗiyyar Najeriya.

  1. Cif MKO Abiola
  2. Kudirat Abiola
  3. Janar Shehu Musa Yar’Adua
  4. Pa Alfred Rewane
  5. Chif Anthony Enahoro
  6. Chif Abraham Adesanya
  7. Commodore Dan Suleiman
  8. Chif Arthur Nwankwo
  9. Chif Chukwuemeka Ezeife
  10. Admiral Ndubuisi Kanu
  11. Chif Frank Kokori
  12. Chif Bola Ige
  13. Chif Adekunle Ajasin
  14. Chif Ganiyu Dawodu
  15. Chif Ayo Fasanmi
  16. Chief Gani Fawehinmi
  17. Chief Olabiyi Durojaiye
  18. Dakta Beko Ransome-Kuti
  19. Chima Ubani
  20. Janar Alani Akinrinade
  21. Farfesa Bolaji Akinyemi
  22. Farfesa Wole Soyinka
  23. Chif Ralph Obioha
  24. Chif Cornelius Adebayo
  25. Olisa Agbakoba
  26. Femi Falana
  27. Abdul Oroh
  28. Sanata Shehu Sani
  29. Gwamna Uba Sani
  30. Chif Olu Falae
  31. Chif Ayo Adebanjo
  32. Chif Ayo Opadokun

Karanta jawabin Tinubu a nan kasa:

An gano kura-kurai a taken Najeriya

A wani labarin, mun ruwaito cewa shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya ba hukumar wayar da kan jama'a ta kasa (NOA) umarnin yin gyara a sabon taken Najeriya.

Kara karanta wannan

Jerin ranakun da Musulmai za su yi hutu a watannin Yuni/Yulin 2024

Shugaban majalisar dattawa ya gano wasu kura-kurai a ɗangwaye na uku, biyar da 18 na sabon taken ƙasar wanda hukumar NOA ta gabatar a makon jiya.

Haka zalika, Sanata Godswill Akpabio ya zargi hukumar da gabatar da kasafin da ba shi ne majalisar tarayya ta amince da shi ba yana mai kira ga NOA da ta gaggauta gyara kurakuran.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Online view pixel