Gobara Ta Tashi a Kwalejin Fasaha a Jihar Kano, Wuta Ta Jawo an Tafka Asara Mai Yawa

Gobara Ta Tashi a Kwalejin Fasaha a Jihar Kano, Wuta Ta Jawo an Tafka Asara Mai Yawa

  • Wata mummunar gobara ta tashi a kwalejin fasaha ta jihar Kano da safiyar yau Talata, inda ta jawo asarar dukiya mai tarin yawa
  • An ruwaito cewa gobarar ta babbake kafatanin sashen koyon Arts and Industrial na kwalejin da ke a bangaren koyon fasaha na kwalejin
  • Kakakin hukumar kashe gobara na Kano, Saminu Abdullahi wanda ya tabbatar da lamarin ya ce har yanzu ba a gano musabbabin wutar ba

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Jihar Kano - An tashi cikin wani mummunan yanayi a jihar Kano bayan da wata gobara ta babbake ilahirin bangaren koyon ilimin fasaha da ke a cikin kwalejin fasaha ta Kano.

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano
Gobara ta kone ajujuwa da ofisoshi a kwalejin fasaha ta Kano. Hoto: @Fedfireng
Asali: Facebook

Rahotanni sun bayyana cewa gobarar ta babbake kafatanin sashen koyon ilmin fasaha da na masan'antu na kwalejin a safiyar yau Talata.

Kara karanta wannan

"An maida rai ba komai ba," Atiku ya riga shugaban kasa ta'aziyyar kisan Katsina

Jaridar Daily Trust ta ruwaito kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Yusif Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gobara ta babbake kwalejin Kano

Saminu Abdullahi wanda ya ce har yanzu ba a gano musabbabin tashin gobarar, ba ya ce wutar ta lakume dukiya mai yawa amma ba a kammala tantance wa ba.

A cewarsa hukumar ta samu kiran gaggawa daga wani Faisal Dauda wanda ya ba da rahoton cewa an samu tashin gobara a kwalejin fasahar.

Mista Saminu ya bayyana cewa ginin mai dauke da ajujuwa tara da ofisoshi shida ya lalace gaba daya.

Kakakin hukumar kashe gobarar ya yi nuni da cewa ba a samu asarar rayuka ba, kuma ana ci gaba da binciken musabbabin wutar.

Gwamnatin Kano za ta biya Doguwa N25m

A wani labarin, mun ruwaito cewa wata babbar kotu da ke jihar Kano ta umarci gwamnatin jihar Kano da ta biya Alhassan Ado Doguwa diyyar Naira miliyan 25.

Kara karanta wannan

Kano: Kwankwaso ya fadi abin da ya dauke hankalin Abba a shekara 1 na mulki

A cikin takardar hukuncin da kotun ta yanke mai lamba FHC/ABJ/ABJ/CS/714/2019, an wanke Hon. Ado Doguwa daga zargin kisan kai.

Wannan na zuwa ne bayan da gwamnatin NNPP a Kano ta gurfanar da Doguwa a gaban kotu ne kan zargin mutuwar mutane akalla 15 a zaben zaben shugaban kasa na 2023.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Online view pixel