Mafi Karancin Albashi: ’Yan Najeriya Sun Gano Tushen Matsalolin Kasa, Sun Ambaci Suna

Mafi Karancin Albashi: ’Yan Najeriya Sun Gano Tushen Matsalolin Kasa, Sun Ambaci Suna

  • Yayin da gwamnatin Najeriya ke bayyana amincewa da kara albashin ma’aikata, gwamnoni sun zama babbar matsala ga jihohinsu
  • ‘Yan Najeriya sun bayyana kuka kan yadda gwamnoni ke korafin ba za su iya biyan mafi karancin albashin N60,000 ba
  • An shawarci NLC da ta ki amincewa da albashin, lamrin da ake sa ran zai kawo sauyi ga goben ma’aikata a Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Najeriya - Gwamnonin jihohi 36 na tarayyar Najeriya a jiya Juma’a 7 ga watan Yuni sun yi watsi da shawarar gwamnatin tarayya na ba ma’aikata N60,000 matsayin mafi karancin albashi.

Daraktan watsa labarai da hulda da jama'a na kungiyar gwamnonin Najeriya (NGF), Hajiya Halimah Salihu Ahmed ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar.

Wannan na zuwa ne a yayin da 'yan Najeriya ke jiran kammala tattaunawar gwamnati da kungiyar kwadago kan sabon mafi karancin albashi a kasar.

Kara karanta wannan

NLC: Tsohon hadimin shugaban ƙasa ya kawo mafita kan mafi ƙarancin albashi a jihohi

Gwamnoni ne matsalar Najeriya
An ce gwamnoni ne matsalar Najeriya | Hoto: Presidency
Asali: Twitter

Gwamnoni ne matsalar Najeriya, inji ‘yan kasa

Sai dai, nuna kin amincewa da gwamnonin suka yi ya ja ‘yan Najeriya tofa albarkacin bakinsu kan wannan lamari.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jaridar Daily Trust ta bayyana martanin da wani dan Najeriya mazaunin Abuja ya yi, inda ya ce:

“Babu shaka gwamnonin ne babbar matsalar wannan kasar! Suna cewa ba za su iya biyan N60,000 ba amma suna yin rayuwa mai kyau suna wadaka da kudin jama'a kan abubuwa marasa muhimmanci. Wannan abin takaici ne.”

Ba wannan ne kadai mai martani kan lamarin ba, Legit ta tattauna da wani malamin makarantar sakandare ta gwamnatin jiha da ke Gabukka a jihar Gombe, M.A Sani, inda yace:

“Gaskiya gwamnoni ba sa tsoron Allah. Ai sun iya dauko ayyukan da ba za su amfane mu ba, sai su rage don biyan ma’aikata albashi.”

Kara karanta wannan

'Yan ƙwadago na shirin ɗaukar mataki bayan Gwamnatin Tinubu ta miƙa tayin N62,000

Ta ma’aikata ake, mu leburori an barmu a baya

Wani mazaunin jihar Gombe, Muhammad Rabiu ya bayyana kukansa, inda yace sam ko da an yi karin ba lallai wadanda ba sa aikin gwamnati su amfana ba.

A cewarsa:

“Ma’aikata za su samu kari, mu kuma da muke leburanci sai dai mui ta addu’a. Ga karin haraji ga tsadar rayuwa sannan ba a ma ta mu leburori.”

Tarihin mafi karancin albashi a Najeriya

A tarihin Najeriya, an sha sauya mafi karancin albashi a lokuta mabambanta domin shawo kan lamarin da ya shafi rayuwar ma'aikata.

Rahoton da wakilin Legit Hausa ya tattara ya bayyana yadda a tsawon tarihi aka samu sauyin albashin a karkashin shugabanni da dama.

Kadan daga dalilan sauya albashin akwai tsadar kayayyaki da kuma tabarbarewar tattalin arziki a kasar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.

Online view pixel