Tsohon Gwamnan CBN Ya Shiga Tasku, Kotu Ta Kwace Manyan Kadarorinsa Na N11.1bn

Tsohon Gwamnan CBN Ya Shiga Tasku, Kotu Ta Kwace Manyan Kadarorinsa Na N11.1bn

  • Kotu ta bayar da umarnin wucin gadi na kwace wasu manyan kadarorin maƙudan kuɗi na tsohon gwamnan CBN, Godwin Emefiele
  • Mai shari'a Chukwujekwu Aneke na babbar kotun tarayya mai zama a Legas ne ya bayar da wannan umarnin ranar Laraba, 5 ga watan Yuni
  • Tun farko hukumar yaƙi da rashawa EFCC ta buƙaci kotun ta kwace kadarorin saboda ana tuhumar da kuɗin sata ya mallake su

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Lagos - Babbar kotun tarayya mai zama a jihar Legas ta kwace kadarorin N11.1bn na tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele.

Kotun ta bai wa gwamnatin tarayya umarnin wucin gadi ta karɓe kadarorin da suka kai darajar N11,140,000,000 na Emefiele, tsohon gwamnan CBN.

Kara karanta wannan

Zargin almundahana: Kotu ta yi umarnin buga sammacin shugaban APC, Ganduje a jaridu

Godwin Emefiele.
Kotu ta kwace wasu kadarorin N11.1bn da ake zargin suna da alaƙa da Emefiele Hoto: Mr Godwin Emefiele
Asali: Facebook

Alkali ya karbe dukiyar Godwin Emefiele

Mai shari'a Chukwujekwu Aneke ya bayar da wannan umarni a zaman shari'a na yau Laraba, 5 ga watan Yuni, 2024, kamar yadda The Cable ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Alkalin ya amince da ƙwace manyan kadarorin biliyoyin Naira na Emefiele ne bayan lauyan hukumar EFCC, Rotimi Oyedepo, ya shigar da buƙatar hakan.

Meyasa kotu ta kwace kadarorin?

Babban Lauyan ya shaidawa kotun cewa ana zargin Emefiele da amfani da kuɗin da ya wawura wajen sayan manyan kadarori, kuma jawo wasu ya sa su wakilce shi.

An ce wadannan kadarorin da aka kwace suna cikin manyan Unguwannin masu kuɗi a babban birnin tarayya (FCT), Abuja, Sahara Reporters ta ruwaito.

EFCC ta kuma ambaci sunayen wasu jami’an CBN guda uku, Obayemi Oluwaseun Teben, Akomolafe Adebayo, da Olubunmi Makinde, ta ce sun taimakawa Emefiele.

Kara karanta wannan

Darajar Naira ta ragu, Dalar Amurka ta ƙara tsada a kasuwa a Najeriya

Kotu ta umarci EFCC ta buga labarin

Bayan kwace kadarorin, kotun ta umarci EFCC ta buga labarin a jaridu domin neman masu sayen kadarorin gabanin a gama kwace su gaba ɗaya.

Mai shari'a Aneke ya dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 21 ga watan Yuni domin yanke hukunci kan bukatar kwace su har abada daga hannun Emefiele.

Daraktan CBN ya tona asirin Emefiele

A wani rahoton kuma hukumar EFCC ta gabatar da shaida a gaban babbar kotun Abuja a shari'ar tsohon gwamnan babban banki CBN, Godwin Emefiele.

Tsohon daraktan sashin ayyuka na CBN, Ahmed Umar, ya faɗi yadda Emefiele ya aiwatar da tsarin sauya fasalin Naira ba tare da amincewa ba.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel