Babu Alamun Warware Rikicin Sarautar Kano bayan Ganawar Gwamna Abba da NSA

Babu Alamun Warware Rikicin Sarautar Kano bayan Ganawar Gwamna Abba da NSA

  • Ga dukkan alamu ganawar Gwamna Abba Kabir da Nuhu Ribaɗu ba ta lalubo hanyar warware rikicin sarautar Kano ba
  • Gwamna Abba ya ce ya ziyarci mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro ne domin masa bayani kan halin da ake ciki a jiharsa
  • Sai dai dukkan ɓangarorin biyu ba su bayyana wani mataki da aka ɗauka a taron da nufin warware rikicin sarautar ba

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - A ƴan kwanakin nan Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya gana da mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkikin tsaro, Nuhu Ribaɗu.

Ana ganin wannan ziyara da gwamnan ya kai wa Ribaɗu ba za ta rasa nasaba da dambarwar da ta ƙi ci kuma ta ƙi cinyewa kan sarautar Kano ba.

Kara karanta wannan

"Kano ta kama hanyar kamawa da wuta," Jigo ya buƙaci Tinubu ya dakatar da Gwamna Abba

Gwamna Abba da Nuhu Ribadu.
Alamu sun nuna ba a samu mafita kan rikicin sarautar Kano a ganawar Gwamna Abba da NSA ba Hoto: Abba Kabir Yusuf, Nuhu Ribadu
Asali: Facebook

Kamar yadda Leadership ta ruwaito, alamu sun nuna an tashi wannan ganawa ba tare da lalubo hanyar warware rikicin sarautar Kano ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A halin yanzun dai Muhammadu Sanusi II da Alhaji Aminu Bayero kowa na ikirarin shi ne Sarkin Kano, lamarin da ya kawo ruɗani a tsakanin al'umma.

Dalilin rikicin sarauta a Kano

Gwamnatin jihar Kano ta zartar da wata doka da ta soke masarautu hudu, wadanda gwamnatin Abdullahi Ganduje ta kirkiro tun a 2019 tare da mayar da masarauta ɗaya. 

Jim kaɗan bayan haka kuma Gwamnatin Abba Kabir ya mayar da Muhammadu Sanusi kan karagar sarkin Kano.

Da farko gwamnatin jihar ta zargi Nuhu Ribadu da hannu wajen dawo da Aminu Bayero jihar amma daga baya ta dora laifin a kan jam’iyyar APC da Ganduje.

Kara karanta wannan

"Mun shirya tsaf," 'Yan sanda sun ƙara ɗaukar mataki kan rigimar sarautar Kano

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yanke zuwa ya zauna da Malam Nuhu Ribadu ranar Alhamis da ta gabata.

NSA da Abba sun gaza warware matsalar

Sai dai ofishin NSA ya ki bayyana sakamakon ganawar da aka kwashe sa’o’i ana yi tsakanin jiga-jigan biyu.

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature ya fitar kuma aka rabawa manema labarai a Kano ranar Alhamis ba ta yi magana kan sakamakon taron ba.

A cewar Bature taron wanda ya dauki sama da sa’a guda, ya maida hankali ne kan batun rusa masarautu guda biyar da majalisar dokokin jihar Kano ta yi.

Sanarwan ta tattaro Gwamna Abba na cewa:

"Mun yi tattaunawa ta fahimtar juna tsakanina da mai ba da shawara kan tsaron ƙasa, aikinsa na da matuƙar muhimmanci ga zaman lafiyar kasa. Hakan ya sa na yi masa bayani kan abubuwan da ke faruwa a Kano."

Huɗubar Sanusi II a masallacin Jumu'a

Kara karanta wannan

Aminu Ado: Dalilin kotu na umartar jami'an tsaro su fitar da Sarkin Kano na 15 daga fada

A wani rahoton kuma Sarki Muhammadu Sanusi II ya jagoranci sallar Jumu'a a babban masallacin Ƙofar Kudu a Kano kuma ya yi huɗuba kan imani da Allah.

Basaraken ya bayyana cewa babu wanda zai ja da hukuncin Allah, inda ya ƙara da cewa komai ka ga ɗan adam ya samu ko ya rasa daga Allah ne.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel