Tinubu Ya Burma Matsala, Lauyoyi Za Su Maka Shi a Kotu Kan Wani Kuskuren da Ya Tafka

Tinubu Ya Burma Matsala, Lauyoyi Za Su Maka Shi a Kotu Kan Wani Kuskuren da Ya Tafka

  • Da alamu shugaban kasa, Bola Tinubu ya shiga matsala kan sauya taken Najeriya da ya yi a dai-dai wannan lokaci
  • Kungiyar lauyoyi ta ALDRAP ta shirya maka shugaban a kotu kan rashin bin tsari wurin tabbatar da dokar a Najeriya
  • Wannan na zuwa ne bayan Tinubu ya rattaba hannu kan dokar sauya taken Najeriya wanda ƴan kasar suka kushe

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Kungiyar lauyoyi ta ALDRAP za ta maka Shugaba Bola Tinubu a gaban kotu.

ALDRAP da kungiyoyin kare hakkin al'umma za su maka shugaban a kotu kan sauya taken Najeriya.

Lauyoyi za su maka Tinubu a gaban kotu
Kungiyar Lauyoyi ta ALDRAP za ta shigar da Tinubu kara kotu kan sauya taken Najeriya. Hoto: Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Facebook

Taken Najeriya: Musabbabin maka Tinubu a kotu

Kara karanta wannan

"Shugaba Tinubu ya saba doka", Kungiyar lauyoyi za ta kotu saboda an sauya taken Najeriya

Sakataren kungiyar ALDRAP, Tonye Jaja shi ya tabbatar da haka a yau Juma'a 31 ga watan Mayu, cewar TheCable.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jaja ya ce ba a bi tsari ba wurin ɗaukar matakin da Majalisar ta yi wanda ya saba ka'idar tabbatar da doka, Daily Post ta tattaro.

"Ba a bi tsari ba wurin tabbatar da dokar kamar yadda sashen 60 na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 ya tanadar."
"Kuma ba a gayyaci jama'a ba wurin jin ra'ayinsu da kuma gudunmawarsu kamar yadda aka yi a 1978."
"Babu wata takarda da shugaban kasa ya tura zuwa ga shugabannin Majalisun gida biyu."

- Tonye Jaja

Wannan na zuwa ne bayan Tinubu ya sauya taken Najeriya daga "Arise O Compatriot" zuwa "Nigeria We Hail Thee" a wannan mako da muke ciki.

Ƴan Najeriya da dama sun kushe wannan mataki na Tinubu musamman a daidai lokacin da ake cikin wani irin hali.

Kara karanta wannan

Taken Najeriya: Tinubu ya yi karin haske kan hikimar komawa tsohon taken kasa

Gwamanti ta bukaci a haddace taken Najeriya

A wani labarin, kun ji cewa Hukumar wayar da kan jama'a a Najeriya (NOA) ta bukaci a haddace sabon taken Najeriya cikin kwanaki uku.

NOA ta ba da wannan sanarwa musamman ga jami'anta da ke duka ƙananan hukumomi 774 a fadin Najeriya.

Hakan ya biyo bayan sauya taken Najeriya da Tinubu ya yi daga "Arise O Compatriot" zuwa "Nigeria We Hail Thee" a wanna mako.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.

Online view pixel