Kwana 2 da Karbar Mulki, Sarki Sanusi II Ya Nada Sabuwar ‘Jakadiyar Sarkin Kano’

Kwana 2 da Karbar Mulki, Sarki Sanusi II Ya Nada Sabuwar ‘Jakadiyar Sarkin Kano’

  • Mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya nada Hajiya A’in Jafaru Fagge a matsayin Jakadiyar Sarkin Kano
  • Wannan nadin na zuwa ne kwanaki biyu bayan da Muhammadu Sanusi II ya koma kan karagar sarautar Kano
  • A hannu daya, zanga-zanga ta barke a wasu sassa na jihar Kano inda ake kira ga gwamnati da ta tsige Sarki Sanusi II

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Jihar Kano - Kwanaki biyu da hawa kan kujerar mulki, sabon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya fara yin sauye-sauye ga hadiman cikin fada.

An nada Jakadiyar Sarkin Kano
Sarki Sanusi II ya nada Hajiya A'in Jafaru mukamin ‘Jakadiyar Sarkin Kano’. Hoto: @babarh
Source: Twitter

An nada Jakadiyar Sarkin Kano

A yau Lahadi, muka samu rahoton cewa mai martaba Sanusi II, ya nada Hajiya A’in Jafaru Fagge a matsayin Jakadiyar Sarkin Kano.

Kara karanta wannan

"Ka hakura da zaman Kano": Kungiyar Arewa ta ba Sarki Aminu shawara bayan an tsige shi

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mai tallafawa gwamnan jihar Kano ta fuskar kafofin sada zumunta, Abdullahi I. Ibrahim ya tabbatar da hakan a shafinsa na X.

Abdullahi I. Ibrahim ya wallafa cewa:

"Mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya nada Hajiya A’in Jafaru Fagge a matsayin Jakadiyar Sarkin Kano."

Kalli sanarwar a nan kasa:

Jakadiyar Sarkin Kano: Mutane sun magantu

Mutane sun yi martani kan wannan nadi na jakadiya.

@Usman_Tokari:

"Babu 'capacity' yar siyasa a fada"

@shamsumailowco1:

"Hajiya muna taya murna"

@nazeef___:

"Ba lokaci, Allah kawo namu nadin"

@isah_muaaz:

"Yan kwankwasiyya kuna sharafi wallahi, gwamnati ta ku, masarauta ta ku."

@ibrahimchicago:

"Agaishe ki jakadiya"

Zanga-zanga ta barke a sassan Kano

A wani labarin, mun ruwaito cewa zanga-zangar nuna adawa da mayar da Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II kan kujerar mulki ta mamaye sassan jihar Kano.

A Gaya da Nasarawa inda aka gudanar da zanga-zangar, al’ummar garin sun yi tururuwa a kan tituna domin nuna adawa da dawo da Sanusi II gidan sarautar Kano.

Masu zanga-zangar dai sun zargi gwamnatin jihar da yin amfani da wata manufa ta siyasa wajen rusa sarakunan biyar tare da neman a maido da masarautun nasu da kuma sarkin da aka tsige.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com