Kotu Ta Tube Rawanin Fitaccen Sarki a Najeriya, an Kwashe Shekaru 29 Ana Shari’a

Kotu Ta Tube Rawanin Fitaccen Sarki a Najeriya, an Kwashe Shekaru 29 Ana Shari’a

  • Wata babbar kotu a Najeriya ta tsige Oba Michael Adetunji Oluwole a matsayin Olute na Ute a Ondo da ke Kudu maso Yammacin Najeriya
  • Kotun ta kuma hana sarkin bayyana kansa a matsayin Olute na Ute, amma yana da zabin kalubalantar hukuncin a kotun daukaka kara
  • Mai shari’a Ademola Enikuomehin ya ba da umarnin sake zaɓen wani sarkin daga cikin zuriyar Mai martaba Olule Omoloja a jihar Ondo

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Owo, Ondo state - Wata babbar kotu ta tube rawanin basaraken Owo, Oba Michael Adetunji Oluwole, daga mukamin Sarkin Ute a karamar hukumar Ose (LGA) ta jihar Ondo.

Babbar kotun Ondo ta kori Oba Michael Oluwole
Kotu a jihar Ondo ta tube rawanin Sarkin Ute, Oba Michael Adetunji Oluwole. Hoto: @afamosigwe
Asali: Twitter

An fara shari'ar Sarkin Ute a 1995

Kara karanta wannan

Tattaunawar hadakar Atiku Abubakar da Peter Obi ta fara daukar hankalin APC

An ruwaito cewa Oba Michael Adetunji Oluwole ya shiga takaddamar shari'a game da zamansa sarki tun a shekarar 1995.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito, gidan sarauta na Olule Omolaja ya kalubalanci cancantar babban sojan (mai ritaya) na samun damar hawa karagar mulki a masarautar.

A hukuncin da ya yanke kan karar da Adewumi Fabuluje ya shigar, Mai shari’a Ademola Enikuomehin, a ya soke tsarin zaben da ya dora Oba Oluwole kan karagar mulki.

Sarki Michael zai iya daukaka kara

Mai shari’a Ademola Enikuomehin ya kuma ba da umarnin a gudanar da sabon zaben sarki na masarautar, in ji rahoton FRCN.

Alkalin kotun ya umurci Oluwole da ya daina bayyana kansa a matsayin basaraken garin.

Mai shari'an ya kara da cewa za a zabi sabon sarki ne daga zuriyar Olule Omoloja kadai.

Kara karanta wannan

Fitattun 'yan Arewa guda 5 da Bola Tinubu ya ba manyan mukamai a jami'o'i

Legit.ng Hausa ta fahimci cewa, korarren sarkin yana da zabin kalubalantar hukuncin da babbar kotun ta yanke a kotun daukaka kara.

Za a gyara dokar Sarakunan Kano

A wani labarin, mun ruwaito cewa majalisar jihar Kano ta fara shirin gyara dokar Sarakunan Kano da Abdullahi Ganduje ya yi amfani da ita wajen tsige Sarki Sanusi II a 2019.

Shugaban masu rinjaye kuma mai wakiltar mazabar Dala, Hussien Dala, ya gabatar da kudirin a gaban majalisar wanda aka amince da shi.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

Online view pixel