Hukumar EFCC ta Musanta yi wa Tsohon Gwamnan APC Bita da Kulli a Shari'ar N80bn
- Shugaban hukumar EFCC, Ola Olukayide ya musanta cewa ya na yiwa tsohon gwamnan Kogi, Yahaya Bello bita-da-kulli
- Ola Olukayide ya bayyana cewa shi ma gadar fayil din binciken ya yi, wanda tuni ya gano akwai matsaloli kuma dole ayi bincike
- Ya bayyana cewa idan ba a binciki badakalar da ake zargin Yahaya Bello da yi ba, ba za a iya bincikar kowa ba
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Abuja-Shugaban hukumar EFCC, Ola Olukayide ya musanta zargin cewa shi ne ya fara bincikar tsohon gwamnan Kogi, Yahaya Bello.
A tattaunawarsa da manema labarai a ranar Talata a Abuja, shugaban hukumar ya ce shi ma gadar binciken ya yi daga tsohon shugaban hukumar.

Kara karanta wannan
Yahaya Bello ya dauki $720,000 ya biya kudin makarantar yaronshi a waje, Shugaban EFCC

Source: Facebook
Shugaban ya ce ba shi da dalilin yi wa Yahaya Bello bita da kulli, kamar yadda Premium Times ta wallafa labarin.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
“ Ba ni na fara binciken ba; gadar fayil din binciken na yi. Na kuma nemi a kawo min shi, na ce akwai matsala a nan,”
- Ola Olukayede
"Mun samu nasarori" Inji EFCC
Ola Olukayode ya kara da cewa ya na kishin ganin an samu ci gaba a Najeriya, wanda a cikin watanni shidan fara aikinsa, hukumar ta kwato Naira biliyan 120 daga hannun ‘yan damfara.
Ya musanta cewa su na aiki da son zuciya tun bayan da ya kama aiki a shekarar 2023, inda ya ce idan ba su bibiyi shari’ar Yahaya Bello ba, ba za su iya bincikar kowa ba, Leadership News ta ruwaito.

Kara karanta wannan
Badakalar $720, 000: Yadda muka yi da tsohon gwamna Yahaya Bello Inji Shugaban EFCC
Shugaban EFCC ya kuma ce sun samu nasara a kotu kan wasu mutane 1600 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban, wadanda tuni aka daure su.
Yahaya Bello na son gurfana gaban kotu
A baya kun ji tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello da yanzu haka ke fuskantar zargin sama da fadi da kudin al’ummarsa ya bayyana cewa ya na son a gurfanar da shi gaban kotu.
Sai dai lauyansa, Adeola Adedipa SAN ya bayyana fargabar umarnin da kotu ta bayar na a cafke shi, inda ya roki kotun ta soke umarnin.
Asali: Legit.ng