Gwamnatin Katsina Ta Karbo Sabon Bashi? Dikko Radda Ya Yi Wa Hukumar DMO Martani
- Gwamnan jihar Katsina, Mallam Dikko Radda ya ce rahoton hukumar kula da basussuka (DMO) kan gwamnatin jihar ba gaskiya bane
- Rahoton ya nuna cewa gwamnatin jihar Katsina na daga cikin jihohin da suka karbi sabon bashi wanda hakan ya kara ta'azzarar bashi a jihohin
- Sai dai da yake martani a cikin wata sanarwar, Gwamna Raddan ya ce tun da ya hau mulkin Katsina bai taba ciwo bashin ko kwabo ba
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Jihar Katsina - Gwamnan Katsina, Mallam Dikko Radda ya musanta rahoton hukumar kula da basussuka ta kasa (DMO) na cewa yana cikin gwamnonin da suka karbo sabon bashi.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/fb07f5db7a1af5c2.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Gwamnatin jihar Sokoto ta ciyo bashin makudan kudi? Gwamna Ahmed ya fayyace gaskiya
![Gwamnan Katsina ya yi magana kan karbo sabon bashi Gwamnan Katsina ya yi magana kan karbo sabon bashi](https://cdn.legit.ng/images/1120/3a505e525534ecbc.jpeg?v=1)
Asali: Twitter
"Har yanzu muna biyan bashi - Radda
Jaridar Leadership ta ruwaito gwamnan a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ibrahim Mohammed ya fitar, ya ce akwai kuskure a rahoton hukumar DMO.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya jadda cewa tun da gwamnatin Radda ta fara mulki a Katsina take biyan basussukan da ta gada daga gwamnatocin baya.
Sanarwar ta kuma ce har yanzu yanzu gwamnatin APC mai ci a jihar Katsina karkashin Gwamna Radda ba ta ciwo bashin ko kwabo ba.
Gwamnatin Radda ta karbo sabon bashi?
A cewar sanarwar:
"Kuma ba wai mun ce gwamnatin jihar ba za ta ciwo bashi nan gaba ba, za ta iya yin hakan a duk lokacin da bukata ta taso.
"Amma a halin yanzu, babu wanda ke bin gwamnatin mu bashi. Yayin da muke kokarin kamanta gaskiya da adalci, muna ba da hajuri ga wadanda wannan rahoto ya bata wa rai."
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/57b6366837101c9d.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Jerin sabbin gwamnonin Arewa 7 da suka karbi bashin biliyoyi cikin watanni 6 kacal
Jaridar This Day ta rahoto Gwamna Radda yana kira ga kafofin watsa labarai da su goyi baya tare da tallafa wa gwamnatin jihar a kokarinta na inganta rayuwar 'yan jihar.
Sanarwar ta kuma kara jaddada manufofin gwamnatin APC a jihar Katsina na samar da ayyukan more rayuwa da saukaka wa jama'a.
Radda ya gwangwaje ma'aikatan Katsina
A wani labarin, Legit Hausa ta ruwaito cewa gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda ya ba da umarnin sakarwa ma'aikata N15,000 domin yin hidimar azumi da Sallah.
Gwamnan ya ce a raba kudaden ga ma'aikatan jiha da na kananan hukumomi, domin rage masu radadin matsin tattalin da kasar ke ciki.
Asali: Legit.ng