Sanatan APC Ya Bayyana Yadda Ya Daina Zuwa Makaranta Saboda Ya Burge Ƴan Matan Garinsu

Sanatan APC Ya Bayyana Yadda Ya Daina Zuwa Makaranta Saboda Ya Burge Ƴan Matan Garinsu

  • Sanata Tahir Monguno ya ba da labarin yadda ya daina zuwa makaranta domin ya riƙa burge ƴan mata a garinsu da ke jihar Borno
  • Monguno, mai wakiltar Borno ta Arewa ya bayyana haka yayin da yake jawabi a zauren majalisar dattawa kan kudirin yaran da ba su zuwa makaranta
  • A cewarsa, domin ya zama ɗaya daga cikin waɗanda ƴan mata suka fi so a al'adar garinsu ne ya ɗauki wannan mataki lokacin yana firamare

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Borno - Sanata mai wakiltar Borno ta Arewa, Tahir Monguno, ya ce ya daina zuwa makaranta a lokacin da yake karatun firamare saboda yana son ya zama abin sha'awa ga 'yan mata a yankinsa.

Kara karanta wannan

Abin da Bola Tinubu ya faɗawa sanatoci a wurin buɗa bakin azumin watan Ramadan a Villa

Monguno, 'dan jam'iyyar APC ya ce al'adar ƙauyensu ce ta sa ya daina zuwa makaranta domin ya ja hankalin ƴan mata.

Sanata Tahir Monguno.
Sanatan Borno ya ce ƴan mata suka sa ya daina zuwa makaranta Hoto: Tahir Monguno
Asali: Facebook

A cewarsa, al'adar ta bai wa mata damar zaɓo mazan da suke direbobi domin su yi nishaɗi da rawa tare da su a wannan lokaci, kamar yadda Premium Times ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ce domin ya zama daya daga cikin wadanda ‘yan matan suka fi so su yi rawa da nishadi da su shiyasa ya daina zuwa makarantar firamare ya kama tuƙi a ƙauyensu.

Sanata Monguno ya ba da wannan labarin ne a zauren majalisar dattawa lokacin da yake ba da gudummuwa a kudirin da Sanata Adebule Oluranti (APC, Legas ta Yamma) ya gabatar.

Kudirin dai ya bukaci majalisar dattawan ta lalubo hanyoyin daƙile ƙaruwar yaran da ba su zuwa makaranta a Najeriya.

Kara karanta wannan

Ramadan: Magidanci ya bayyana yadda yake tafiya mai nisa don samun abincin buda baki ga iyalansa

'Dalilin daina zuwa makaranta'

"Na yanke cewa wani abu a wannan kudirin ne saboda abin da ya faru a rayuwata lokacin da nake tasowa. Lokacin ina aji 7 a firamare, bisa ra'ayin kaina na daina zuwa makaranta.
"Dalilin da ya sa na daina zuwa makaranta shi ne saboda a garin mu a wancan lokacin kowa so yake ya zama direba, da zaran ka zama direba shikenan ka zama ɗaya daga cikin manyan gari.
"Muna da wata al'ada a lokacin, a al'adar maza da mata za su zo suyi layi, ƴan mata za su zaɓi mazan da za su yi rawa da su. To matan direbobi kaɗai suke ɗauka, ba ruwansu da mu.
"Ganin hake na ce tun da haka abin yake bari na koma na zama direba saboda idan an zo wurin wannan wasan mata su zaɓe ni mu yi rawa. Saboda haka na daina zuwa makaranta."

- Tahir Monguno.

Kara karanta wannan

Kotu ta yanke hukunci kan mutumin da ya sace Alkur'anai a Masallaci, ta ba shi zaɓi 1 a Abuja

Meyasa sanatan ya ba da labarin?

Monguno, wanda a yanzu ya zama lauya, ya ce ya yi sa'ar komawa makaranta domin kawunaa ne ya dage cewa dole ne ya samu ilimin zamani.

Sanatan ya ba da labarin rayuwarsa ta farko ne domin nuna rashin dacewar yaran da ke barin karatun boko don biyan wasu bukatusu na daban, rahoton jaridar Tribune.

Tinubu ya sha ruwa da sanatoci

A wani rahoton kuma Bola Ahmed Tinubu ya lashi takobin cewa gwamnatinsa ba za ta zura ido ta yi shiru ba kan kisan dakarun sojoji a jihar Delta.

Yayin da ya karɓi bakuncin sanatoci a wurin buɗa baki, Tinubu ya ce waɗanda suka kashe sojoji a Okuama za su ɗanɗana kuɗarsu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262