Auren Bogi: EFCC Ta Maka Matashi a Kotu Kan Damfarar Masoyiyarsa Ba’amurkiya $373,000

Auren Bogi: EFCC Ta Maka Matashi a Kotu Kan Damfarar Masoyiyarsa Ba’amurkiya $373,000

  • EFCC ta kwato $13,204 daga wajen wani 'dan Najeriya da ke fuskantar shari'a kan damfara ta yanar gizo da kitsa auren bogi da wata Ba'amurkiya, da ya yi ikirarin masoyiyarsa ce
  • An fara gurfanar da Nwachi Chidozie Kingsley a gaban wata kotun babbar birnin tarayya, Maitama, Abuja a watan Maris din 2023 kan aikata damfara ta yanar gizo
  • Da ya gurfana a gaban kotu a ranar Talata, 13 ga watan Fabrairu, wanda ake tuhumar, ya fada ma Mai shari'a Kekemeke cewa EFCC ta samu wani fili daga wajensa da motoci

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

FCT, Abuja - An gurfanar da wani mutum mai suna Nwachi Chidozie Kingsley, kan zargin damfarar wata Ba'amurkiya, Nicole Kierulff Sayers kudi $373,000 kan yaudarar cewa zai aureta.

Kara karanta wannan

Hatsabibin 'dan bindiga da ya addabi jihar Arewa, Kachalla Duna, ya shiga hannu

Okanne Kelechi, ya bayyana haka a ranar Talata, 13 ga watan Fabrairu, 2024, yayin da yake bayar da shaida a gaban Mai shari'a U.P Kekemeke na babban kotun tarayya, Maitama, Abuja.

Matashin ya damfari masoyiyarsa Ba'amurkiya
Auren Bogi: EFCC Ta Maka Matashi a Kotu Kan Damfarar Masoyiyarsa Ba’amurkiya $373,000 Hoto: @officialEFCC
Asali: Twitter

Yadda aka damfari Nicole Kierulff Sayers

Jami'an hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) ne suka kama Kingsley a watan Mayun 2022, a wani wuri a Abuja bayan bayanan sirri ya nuna cewa yana damfara ta yanar gizo.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban sashin labarai na EFCC, Dele Oyewale ya tabbatar da ci gaban a wata sanarwa da ya wallafa a shafin X na hukumar, tare da hotuna.

Hukumar ta yi karin haske kan yadda 'dan damfarar ya yaudari masoyiyarsa Ba'amurkiya sannan ya damfare ta.

Hukumar EFCC ta bayyana cewa mai gabatar da kara na biyu, Okanne Kelechi, ya shaida wa mai shari’a U.P. Kekemeke cewa Shugaban sashen damfarar kudade ya samu bayanan sirri inda bayan nan aka dauki matakin.

Kara karanta wannan

"Ya dauki nauyin kawunnai na 10 zuwa Hajji": Tambuwal ya tuna haduwarsu ta karshe da Wigwe

Wasu abubuwa aka kwato daga hannun matashin?

Kelechi, jami'in EFCC, ya bayyana cewa jami'an hukumar sun samo wani fili, wani tagwayen gida a No 1, Kemme Close, off NTA Road, kusa da cocin Royal Int’l Port Harcourt, jihar Ribas, kudi $13,204, motocin Lexus Ex 350 da Toyota Venza.

Shaidan, wanda lauyan masu gabatar da kara, Fatsuma Muhammad ta jagoranta, ya bayyana cewa daga cikin hujjar da ake da su kan wanda ake tuhuma akwai"shafukan damfara daban-daban a Linkedin wadanda ya yarda cewa shi ya bude su."

Ya kuma fada ma kotu cewa martani daga ma'aikatar ayyuka da gidaje ya nuna cewa kwangilar ba na gaskiya bane,

Haka kuma wanda ake tuhumar ya yarda cewa ya aikewa Sayers da wasu 'yan kasar waje da ya damfara wasikar samun kwangila na bogi.

Mai shari’a Kekemeke ya dage sauraron karar har zuwa ranar 30 ga Afrilu, 2024 domin ci gaba da shari’ar.

Kara karanta wannan

Tashin Hankali Yayin da Wani Mummunan Ibtila'i Ya Faru a Hedkwatar APC Ta Ƙasa a Abuja

An hukunta Mama Boko Haram kan zambar N40m

A wani labarin kuma, mun ji cewa kotu ta kama Aisha Alkali Wakili wacce aka fi sani da Mama Boko Haram da aikata laifi.

A ranar Litinin, 12 ga watan Fubrairu 2024, hukumar EFCC ta sanar da yin nasara a shari'ar da take yi da ita.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng