Babbar Kotu Ta Yanke Hukunci Kan Tsohon Ministan Da Ake Zargi Da Karkatar Da $6bn

Babbar Kotu Ta Yanke Hukunci Kan Tsohon Ministan Da Ake Zargi Da Karkatar Da $6bn

  • Babbar kotun Abuja ta bada belin tsohon ministan wutar lantarki, Olu Agunloye, kan kuɗi Naira miliyan 50 ranar Alhamis
  • Hukumar EFCC ta gurfanar da Mista Agunloye gaban ƙuliya ne kan zargin damfara a kwangilar tashar wutar mambila
  • Alkalin kotun ya amince da belin amma ya karɓe farfo ɗin tsohon ministan kuuma ya gindaya masa sharuɗɗa

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Babbar kotun birnin tarayya Abuja ta ba da belin tsohon ministan wutar lantarki da ƙarafa, Olu Agunloye, kan kudi Naira miliyan 50.

Alkalin kotun, mai shari'a Jude Onwuegbuzie, shi ne ya amince da bada belin tsohon ministan a zaman ranar Alhamis, 11 ga watan Janairu, 2024, Channels tv ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Kotun Koli ta yanke hukuncin karshe kan takaddamar zaben gwamnan PDP, NNPP ta gurza kasa

Tsohon ministan wutar lantarki, Agunloye.
Kotu ta bada belin tsohon ministan wutar lantarki kan Naira miliyan N50m Hoto: Olu Agunloye
Asali: Twitter

An gurfanar da Agunloye ne a gaban kuliya bisa tuhume-tuhume bakwai da suka shafi bada kwangilar damfara da kuma almundahana a hukumance, ranar Laraba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, na binciken Agunloye kan kwangilar samar da wutar lantarki ta Mambilla ta dala biliyan 6.

Bayan gurfanar da shi, Alkalin kotun ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare shi a gidan gyaran halin Kuje har zuwa lokacin da za a saurara tare da yanke hukunci kan neman beli.

Yadda zaman kotu ya gudana

Da yake gabatar da bukatar, Lauyan tsohon ministan, Adeola Adedipe, ya roki kotu da ta bayar da belin wanda yake karewa bisa la'akari da sanayya ko kuma sassauci.

Ya ce Argunloye ba mutum ne mai ƙafar yawo ba kuma masu gabatar da kara sun gurfanar da shi ne sakamakon rashin fahimta da rashin sani.

Kara karanta wannan

Nesa ta zo kusa: Kotun koli ta sanya ranar yanke hukuncin kan zaben gwamnan Kano, Bauchi da wasu jihohi 5

Adedipe ya kuma roki kotu da kada ta bada umarnin a yi amfani da ma’aikacin gwamnati a matsayin wanda zai tsayawa wanda yake karewa yayin bada belin.

Sai dai lauyan masu gabatar da ƙara ya nuna rashin aminta da buƙatar bada belin tsohon ministan, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Hukuncin da kotu ta yanke

Da yake yanke hukuncin kan buƙatar belin, mai shari’a Onwuegbuzie ya ce ra'ayin kotun ya karkata ga bayar da belin wanda ake tuhuma.

Ya bayar da belin wanda ake tuhuma kan Naira miliyan 50, sannan ya umarce shi da ya gabatar da mutum biyu da za su tsaya masa.

Alkalin ya kuma umarci tsohon ministan ya miƙa fasfo ɗinsa ga kotun kuma dole ya halarci dukkan zaman da za a yi a shari'ar. Daga nan ya ɗage zaman zuwa 12 ga watan Fabrairu.

Gwamnonin APC sun sa labule a Abuja

Kara karanta wannan

Betta Edu: Kwanaki da dakatar da Minista, an gano Naira Biliyan 50 da ICPC ta bankado

A wani rahoton na daban Ƙungiyar gwamnonin jam'iyyar APC na ganawar sirri yanzu haka a masaukin gwamnan jihar Imo da ke Asokoro a birnin tarayya Abuja

An gano cewa shugaban ƙungiyar gwamnonin kuma gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma ne ke jagorantar zaman yau Alhamis.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel