Gwamnatin Tinubu Ta Amince da Kamfanonin Jiragen Sama 3 da Zasu Yi Jigilar Maniyyata Hajjin 2024

Gwamnatin Tinubu Ta Amince da Kamfanonin Jiragen Sama 3 da Zasu Yi Jigilar Maniyyata Hajjin 2024

  • Gwamnatin tarayya ta ware kamfanonin sufurin jiragen sama 3 da zasu yi aikin jigilar maniyya a aikin hajjin bana 2024
  • Hukumar jin daɗin alhazai ta ƙasa (NAHCON) ce ta sanar da sunayen tare da kamfanonin jiragen da zasu yi jigilar kayan alhazai
  • NAHCON ta raba wa kowane kamfani johohin da zai yi aiki, inda ta bai wa kamfanin Max Air kaso mafi tsoka

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Gwamnatin Najeriya karkashin shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ta amince da kamfanonin jiragen sama guda uku da za su yi jigilar maniyyata aikin Hajji na 2024.

Kamfanonin jiragen da aka amince da su sune Air Peace Ltd., Max Air da kuma kamfanin sufurin jiragen sama na FlyNas na Saudiyya, kamar yadda Leadership ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Don burge Bankin Duniya: An tona asirin dalilin Tinubu na kara farashin mai da wutar lantarki

Jirgin kamfanin Air Peace.
Gwammatin Tinubu Ta Amince da Kamfanonin Jirage 3 da Zasu Yi Jigilar Maniyyatan 2024 Hoto: Air Peace
Asali: Facebook

Haka nan kuma gwamnatin Tinubu ta amince da kamfanonin dakon kaya waɗanda zasu yi jigilar kwaso kayayyakin alhazan Najeriya a aikin hajjin bana.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kamfanonin jiragen dakon kayan da aka amince da su sune, Cargo Zeal Technologies Ltd, Nahco Aviance da kuma Qualla Investment Limited.

Wannan na kunshe ne a wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun Fatima Sanda Usara, mataimakiyar daraktan yaɗa labarai na hukumar jin daɗin alhazai ta ƙasa (NAHCON).

Yadda aka rabawa kamfanonin sufurin aiki a hajjin 2024

Sanarwan ta ce kamfanin Air Peace zai yi jigilar maniyyata daga jihohin Abia, Akwa Ibom, Anambra, Bayelsa, Kuros Riba, Delta, Ebonyi, Edo, Ekiti, Enugu, Imo, Kwara, Ondo da Ribas, da kuma babban birnin tarayya Abuja.

Kamfanin jirgin saman Saudiyya FlyNas zai yi jigilar maniyyata daga jihohin Borno, Legas, Osun, Ogun, Neja, Sakkwato, Kebbi, Yobe da Zamfara, Daily Trust ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Dangote ya kara shiga matsala bayan hukumar EFCC ta ba shi sabon umarni

Yayin da Max Air da ke da kaso mafi tsoka zai yi jigilar alhazai daga jihohin Bauchi, Benuwe, Kano, Katsina, Kogi, Nasarawa, Adamawa, Oyo, Taraba, Kaduna, Gombe, Jigawa da Filato.

Tinubu Ya Faɗi Babban Haɗari 1 Tal da Ke Tunkaro Najeriya

A wani rahoton na daban Bola Ahmed Tinubu ya hango babban haɗari na tunkaro Najeriya idan har ba a magance matsalar ƴan bindiga ba.

Shugaban kasar ya ce burin haɗa tattalin arzikin dala tiriliyan ɗaya ka iya shiga babban haɗari idan jami'an tsaro ba su yi da gaske ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262