An Shiga Jimami Bayan Rasuwar Addar Tsohon Gwamna a Najeriya, Bayanai Sun Fito

An Shiga Jimami Bayan Rasuwar Addar Tsohon Gwamna a Najeriya, Bayanai Sun Fito

  • Addar tsohon gwamnan Osun, Prince Olagunsoye Oyinlola ta rasu ta na da shekara 87 a duniya a yau Alhamis
  • Marigayiyar Victoria Moradehun Popoola ta kasance kamar uwa a wurin tsohon gwamnan bayan rasuwar mahaifiyarsa
  • Popoola wacce ungozoma ce ta yi ritaya kuma ta kasance babbar ƴa a cikin iyalan Oba Moses Oyinlola

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Osun - Tsohon gwamnan jihar Osun, Prince Olagunsoye Oyinlola ya rasa addarsa.

Marigayiyar Victoria Moradehun Popoola ta rasu ta na da shekaru 87 a duniya a yau Juma'a 29 ga watan Disamba.

Addar tsohon gwamna a Najeriya ta riga mu gidan gaskiya
An sanar da rasuwar yar uwar tsohon gwamnan jihar Osun, Oyinlola. Hoto: Prince Olagunsoye Oyinlola.
Source: Facebook

Wace ce marigayiya Victoria a wurin Oyinlola?

Popoola wacce ungozoma ce da ta yi ritaya ita ce babbar ƴa a wurin mahaifiyarsa, cewar Tribune..

Kara karanta wannan

2024: Kwanaki 2 da mutuwar gwamna, Lucky ya manta da shi ya ziyarci Tinubu kan wani babban dalili

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Marigayiyar ta kasance uwa a wurin Oyinlola bayan rasuwar mahaifiyarsu a shekarar 1959 lokacin ya na shekara takwas.

Victoria ta yi aiki a jihar Sokoto lokacin da tsohon gwamnan ya shiga aikin soja a shekarar 1969.

Wannan na zuwa ne kwanaki biyu bayan rasuwar gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu a kasar Jamus, cewar IRepoteronline.

Wane martani tsohon gwamnan ya yi kan rasuwar?

Tsohon gwamnan ya bayyana mutuwar marigayar a matsayin karshen iyalan Oba Moses Oyinlola.

Ya bayyana marigayar a matsayin uwa ta biyu a gare shi wacce ta dauki nauyin karatunsa da rayuwarsa tun ya na karami.

Daga cikin wadanda suka tura sakon ta'aziya akwai tsohon mataimakinsa, Erelu Olusola Obada inda ya bayyana rasuwar a matsayin babban rashi.

A cikin makon na da muke ciki an samu mace-macen manyan mutane masu mukami a Najeriya da dama.

Daga cikinsu akwai tsohon kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Umar Na'Abba da Gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu.

Kara karanta wannan

Karin hadiman gwamna 2 sun yi murabus daga muƙamansu, sun bayyana babban dalili

Ghali Na'Abba ya riga mu gidan gaskiya a Abuja

A wani labarin, da safiyar Laraba ce 27 ga watan Disamba aka wayi gari da rasuwar tsohon kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Umar Na'Abba.

Na'Abba ya rasu a wani asibiti da ke birnin Tarayya, Abuja bayan fama da doguwar jinya.

Da yammacin ranar ce aka binne mamacin da misalin karfe 5:38 na yamma a Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.