Jimami Yayin da Babban Mai Sarautar Gargajiya Ya Rasu Ya Na da Shekaru 61 a Duniya, Bayanai Sun Fito
- An shiga jimami bayan rasuwar mai sarautar gargajiya a kauyen Umunya da ke karamar hukumar Oyi a jihar Anambra
- Marigayin Chris Onyekwuluje da ke sarautar yankin Umunya ya rasu ya na da shekaru 61 bayan fama da jinya
- Shugaban yankin, Cif Innocent Nwabueze ya bayyana mutuwar masaraucin gargajiyar a matsayin abin takaici
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.
Jihar Anambra – Babban mai sarautar gargajiya a jihar Anambra ya rigamu gidan gaskiya a yau Alhamis 28 ga watan Disamba.
Marigayin Chris Onyekwuluje da ke sarautar yankin Umunya a karamar hukumar Oyi da ke jihar ya rasu ya na da shekaru 61.

Source: Facebook
Yaushe mai sarautar gargajiyar ya rasu?
Chris wanda ya hau karagar mulkin kauyen ne shekaru 25 da suka wuce inda ya rasu a birnin Abuja bayan fama da jinya, cewar The Nation.

Kara karanta wannan
Awanni da mutuwar gwamna da tsohon Shugaban Majalisa, an rasa mai mulki a Najeriya
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Shugaban yankin, Cif Innocent Nwabueze ya bayyana mutuwar masaraucin gargajiyar a matsayin abin takaici.
Ya ce:
“Dole mu karbi wannan lamari da gaskiya, shugabanmu ya tafi, yaushe zai dawo wannan ba mu sani ba, amma abin bakin ciki ne a gare mu.”
Rahotanni sun tabbatar da cewa marigayin ya rasu ne bayan fama da jinyar ciwon daji na tsawon lokaci, cewar Platinum Post.
Wata majiya ta ce:
“Duk da bai yi wani abin banza a kauyen ba, amma mutuwarshi ba wanda za a yada a kafafen sadarwa ba ce.
“Kauyen Umunya ta na da tsarin sanar da dukkan wata mutuwa musamman da masu sarautar gargajiya.”
Marigayin ya sanu musamman a lokacin mulkin tsohon gwamnan jihar Anambra, Chinwoke Mbadinuju.
A kwanakin nan ya fada wa mutanen kauyen cewa zai mulke su har na tsawon shekaru 100.
Wannan furuci na shi ya fusata dattawan yankin wadanda suka nuna fushinsu a fili kan kalaman marigayin.

Kara karanta wannan
Akeredolu: Tinubu ya girgiza da mutuwar gwamnan Ondo, ya tura sako ga gwamna mai jiran gado
Tsohon gwamna Akeredolu ya rasu
A wani labarin, tsohon gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu ya rasu a jiya Laraba 27 ga watan Disamba.
Akeredolu ya rasu ne a kasar Jamus bayan fama da jinya ta cutar daji na tsawon lokaci a Jamus.
Daga bisani, an rantsar da mataimakinsa, Lucky Aiyedatiwa da misalin karfe hudun ranar Larabar a birnin Akure.
Asali: Legit.ng