Shugaban Gwamnonin Najeriya Ya Yi Magana Kan Rasuwar Gwamnan Jihar Ondo Na APC

Shugaban Gwamnonin Najeriya Ya Yi Magana Kan Rasuwar Gwamnan Jihar Ondo Na APC

  • Shugaban NGF kuma gwamnan jihar Kwara ya yi ta'aziyyar rasuwar Gwamna Akeredolu na jihar Ondo
  • Gwamma AbdulRazaq ya ce bayyana marigayin a matsayin dattijon ƙasa kuma wanda ba za a taɓa mantawa da shi ba
  • Ya kuma yi ta'aziyya ga gwamnati da al'ummar jihar Ondo da kuma iyalansa, inda ya masa fatan samun salama

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kwara - Shugaban ƙungiyar gwamnonin Najeriya (NGF) kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya yi magana kan rasuwar Gwamna Olurotimi Akeredolu (SAN) na jihar Ondo.

Shugaban gwamnonin ya bayyana alhini da jimamin rasuwar Gwamna Akeredolu, wanda Allah ya yi wa rasuwa bayan fama da doguwar jinya.

Gwamnan Kwara ya yi ta'aziyyar rasuwar Akeredolu.
Shugaban NGF, Gwamna Abdulrazaq Ya Yi Ta'aziyar Rasuwar Gwamnan Ondo Hoto: Abdulrahman Abdulrazaq, Olurotimi Akeredolu (SAN).
Asali: Facebook

Kara karanta wannan

Bayan mutuwar Akeredolu, jigon APC ya bayyana wanda za a rantsar a matsayin sabon gwamnan Ondo

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Gwamna AbdulRazaq ya kuma aike da sakon ta'aziyya ga kungiyar gwamnonin APC, al'ummar jihar Ondo da kuma iyalan marigayin bisa wannan babban rashi.

Bugu da ƙari, ya yi ta'aziyya ga ƙungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA) bisa rasuwar gwamnan, wanda ya kasance tsohon shugabanta, kamar yadda The Nation ta ruwaito.

Shugaban NGF ya tura sakon ta'aziyya

Ya bayyana marigayi gwamnan a matsayin dattijon ƙasa wanda ya yi abin da ba za a taba mantawa da shi ba a harkokin aikin gwamnati.

A kalamansa, Gwamna AbdulRazaq ya ce:

“Ina mika ta’aziyya ga kungiyar gwamnonin APC, gwamnati da al’ummar jihar Ondo, kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA), da kuma dangin dan uwana kuma abokin aikina mai girma Olurotimi Akeredolu SAN."
"Lauya ne na sahun gaba kuma hazikin dan siyasa mai kishin ci gaba, za a tuna da shi bisa jajircewarsa, kishin kasa, da gudunmawar da ya bada mara misaltuwa ga tsarin mulki da cigaban siyasar Nijeriya."

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya yabawa gwamnan PDP bayan ya yi muhimmin abu 1

"Duk da mutuwarsa ta sosa rai amma zamu rungumi haƙuri duba da kyawawan ayyukan da ya bari a matsayinsa na mai gaskiya kuma dattijon arziƙi."

Daga ƙarshe, shugaban NGF ya yi addu'ar Allah ya sa ransa a salama kuma ya kula da iyalan gwamnan, waɗanda ya mutu ya bari, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Abubuwan da ya kamata ku sani game da Gwamnan Ondo

A wani rahoton kuma bayan tabbatar da rasuwar gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu, Legit Hausa ta tattaro muku wasu muhimman abubuwa game da shi.

A ranar 13 ga watan Disamba ne Akeredolu ya dauki hutu don neman lafiyarsa inda Shugaba Tinubu ya ba da umurnin mika mulkin jihar hannun mataimakin Akeredolu, Mr Aiyedatiwa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262