Ana Dab da Kirsimeti Shugaba Tinubu Ya Aike da Sako Mai Ratsa Zuciya Ga Yan Najeriya

Ana Dab da Kirsimeti Shugaba Tinubu Ya Aike da Sako Mai Ratsa Zuciya Ga Yan Najeriya

  • Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyaana cewa zai yi adalci ga kowa ba tare da la'akari da bambancin ƙabila ko addini ba
  • Shugaban ƙasar ya bayyana hakan ne a birnin Legas bayan ya yi Sallar Juma'a a masallacin ƙungiyar Ansar-Ud-Deen
  • Tinubu ya yi nuni da cewa yana sane da halin da ake ciki kuma gwamntinsa na aiki tuƙuru domin ragewa ƴan Najeriya raɗaɗi

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Legas - Shugaba Bola Tinubu ya tabbatar da cewa zai kasance mai adalci a koyaushe ga ƴan Najeriya, kuma gwamnatinsa ta jajirce wajen ciyar da haɗin kan Nijeriya gaba da tabbatar da walwala da wadata ga ƴan kasa baki ɗaya.

Ya yi wannan alƙawarin ne a babban masallacin Ansar-Ud-Deen da ke Surulere, Legas, a ranar Juma’a, 22 ga watan Disamban 2023.

Kara karanta wannan

Yan majalisa na son FG ta amince a rika cinikayya da Yuan na kasar Sin, sun bayar da dalilansu

Shugaba Tinubu ya aike da sako ga yan Najeriya
Shugaba Tinubu ya ba yan Najeriya sabon tabbaci Hoto: Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Shugaba Tinubu ya bayyana cewa sauye-sauyen tattalin arziƙi da gwamnatinsa ta ɓullo da su na da nufin samar da tsayayyen tushe mai inganci ga ƴan Nijeriya na yau da masu zuwa nan gaba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar wata sanarwa da Ajuri Ngelale, ya fitar, Tinubu ya gudanar da Sallar Juma'a a masallacin ƙungiyar Ansar-Ud-Deen Society of Nigeria (ADS) inda ya yaba da gudunmawar da suke bayarwa ga addinin Musulunci, da tallafawa marasa ƙarfi.

Ya kuma yi kira ga mambobin da su ci gaba da jajircewa kan manufofinsu na ciyar da ilimin ƴan ƙasa gaba, tare da bunƙasa kyawawan halaye da zamantakewar al’ummar musulmi.

'Sauki na nan tafe' - Tunibu

Da yake nanata ƙudurinsa na kyautata rayuwar ɗaukacin ƴan ƙasa, Shugaba Tinubu, wanda yake takaitaccen hutun Kirsimeti a Legas, ya ce an rage kashi 50 cikin 100 na kuɗin zirga-zirga a tsakanin jihohi a faɗin ƙasar nan, da kuma biyan kuɗaɗen alawus-alawus na masu cin gajiyar N-Power.

Kara karanta wannan

Kungiyar kwadago ta kasa ta yi wa Shugaba Tinubu da CBN babbar barazana kan abu 1 tak

Ya ce ya yi hakan ne domin duk kokarin da ake yi na rage radadin da ƴan Najeriya ke fama da su a wannan kakar bukukuwan, inda ake sa ran kawo sababbi a sabuwar shekara.

Ya ƙara da cewa:

“Mun himmatu wajen tabbatar da yanayi mafi inganci ga ƴan ƙasa ba tare da la’akari da bambancin ƙabila, addini ko yanki ba. Manufofi daban-daban da aka riga aka aiwatar ana sa ran za su kawo babban taimako ga mutanenmu. Mun san ciwon su, kuma muna magance su gaba ɗaya."

Gwamnati Za Ta Saki Sunayen Waɗanda Za a Ba Tallafi

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnatin tarayya ta yi alƙawarin bayyana sunayen mutanen da za su amfana da tallafin N50,000.

Ministar jin ƙai, Dr. Betta Edu ita ce ta yi wannan alƙwarin inda ta ce za a wallafa sunayen ne a cikin watan Janairun 2024.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng