Kakakin Majalisar Wakilai Ya Karanto Sunayen Sabbin Shugabannin Kwamitoci 27 da Mataimaka

Kakakin Majalisar Wakilai Ya Karanto Sunayen Sabbin Shugabannin Kwamitoci 27 da Mataimaka

  • Majalisar wakilan tarayya ta yi gyara a shugabancin kwamitoci 27 yayin da aiki ya fara kankama kan kasafin kuɗin 2024
  • Tajudeen Abbas ya karanto sabbin ciyamomin kwamitocin da mataimakansu biyo bayan tsige wasu yan majalisa da kotu ta yi
  • Ya umarci su gaggauta miƙa ragama ga sabbin domin aikin zama da ma'aikatu da hukumomin gwamnati ya tafi cikin sauƙi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Kakakin majalisar wakilan tarayya, Abbas Tajuddeen, ya karanta sunayen sabbin shugabannin kwamitoci 27 da mataimakansu na majalisar.

Kakakin majalisar wakilan tarayya, Tajudeen Abbas.
Shugaban Majalisa Abbas Ya Sanar da Shugabanni da Mataimaka na Kwamitoci 27 Hoto: HouseNGR
Asali: Twitter

Kwamitocin sun kunshi guda 26 da ake da su a majalisar wakilai ta ƙasa da kuma ƙarin guda ɗaya da aka raɗa wa sunan, "kwamitin abinci da samar da abinci."

Kara karanta wannan

Fitaccen Sarki a arewa ya raba Zakkah ga talakawa marasa galihu 10,000, An bayyana miliyoyin kuɗin

Daily Trust ta tattaro cewa Abbas ya sanar da sabbin shugabannin kwamitocin da mataimakansu a zaman mambobin majalisar na ranar Jumu'a, 1 ga watan Disamba, 2023.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kakakin ya bayyana sauye-sauyen da aka samu a kwamitocin jim kaɗan bayan kasafin kuɗin 2024 ya tsallaka zuwa karatu na biyu a zauren majalisar.

Honorabul Abbas ya karanto sunayen kana ya roƙi shugabanni da mataimaka masu barin gado su hanzarta miƙa ragamar kwamitocin ga sabbin da aka naɗa.

Wannan sauye-sauye na zuwa ne yayin da majalisar wakilan ke shirin fara sauraron ma'aikatu da hukumomin gwamnati waɗanda zasu zo kare kasafinsu.

Da yake jawabi, Abbas ya ce:

"Wannan shi ne jerin sunayen ciyamomin kwamitoci da mataimakansu bayan an gyara su. Akwai buƙatar masu barin gado su mika ragama ga sabbin waɗanda suka maye gurbinsu cikin hanzari."
"Hakan na da matuƙar muhimmanci domin tattabar da zaman da za a fara da ma'aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya ya tafi yadda ya dace."

Kara karanta wannan

Biloniya Abdulsamad Rabiu ya ki karban babban mukami a gwamnatin Tinubu

Meyasa aka samu canji a kwamitocin?

Sake gyaran kwamitocin ya biyo bayan tsige wasu daga cikin ‘yan majalisar da kotun daukaka kara ta yi, Channels tv ta rahoto.

Kusan mambobin majalisar wakilai 15 ne suka rasa kujerunsu wanda hakan ya taba kwamitoci shiyasa aka yi gyara.

APC Ta Bukaci Kowa Ya Bi Yarjejeniyar Zaman Lafiya

A wani rahoton kuma Jam'iyyar APC ta zargi wasu shugabannin NNPP da saɓawa yarjejeniyar zaman lafiyam da suka sa wa hannu a hedkwatar yan sanda.

Mataimakin shugaban APC na Kano, Shehu Maigari, ya ce ya kamata 'yan sanda su ɗauki mataki domin a gabansu kowa ya sa hannu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262