Nasara: Dakarun Sojoji Sun Buɗe Wa Tawagar 'Yan bindiga Wuta, Sun Kashe Su da Yawa a Arewa
- Sojojin rundunar OPSH sun halaka yan bindiga bakwai a ƙaramar hukumar Zangon Kataf da ke jihar Kaduna
- Mai magana da yawun rundunar, Kyaftin Oya James, ya ce sojojin sun kwato muggan makamai daga hannun yan ta'addan
- Ya ce a makon jiya kaɗai, sojojin sun kubutar da mutane 15 da aka yi garkuwa da su kuma sun dakile hare-haren yan bindiga
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Kaduna - Jami'an sojojin rundunar Operation Safe Haven (OPSH) sun samu nasarar murƙushe ƴan bindiga bakwai har lahira a ƙaramar hukumar Zangon Kataf ta jihar Kaduna.

Asali: Twitter
Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, bayan kashe ƴan ta'addan, sojojin sun kwato makamai masu yawa daga hannunsu.
Wannan nasara na ƙunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar sojin OPSH, Kaftin Oya James, ya fitar ranar Talata, 21 ga watan Nuwamba.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya ce yayin da sojojin suka fita sintiri cikin shirin yaƙi, kwatsam suka haɗu da ƴan bindigan a filin Kachallah, inda ba tare da bata lokaci suka buɗe musu wuta aka yi artabu mai tsanani.
A cewarsa, sakamakon musayar wutar ne sojojin suka tura ƴan bindiga shida zuwa lahira kana sauran suka tsere ɗauke da raunukan harsashin bindiga.
A rahoton Guardian, kakakin OPSH ya ce:
“Sojoji sun bincike yankin inda suka kwato bindiga kirar AK 47 guda daya, magazine 2, alburusai 52 mai nauyin 7.62mm, babur daya, wayoyin Tecno 2, fakiti 2 na taba sigari, da wasu alburusai iri-iri."
Dakarun sun kashe wani hatsabibin ɗan bindiga

Kara karanta wannan
Yanzun nan: Atiku Abubakar ya maida martani mai zafi kan tsige gwamnonin arewa biyu
Ya ƙara da cewa sojojin sun yi nasarar kashe wani da ake zargin dan fashi ne, Musa Wada a wani samame da suka kai a kauyen Kondo da ke karamar hukumar Zangon Kataf.
Ya kuma bayyana cewa an kama mutane 33 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a cikin makon da ya gabata.
James ya ce:
“Bugu da kari, an kubutar da mutane 15 da aka yi garkuwa da su, an dakile hare-hare uku da aka kai kauyuka, sannan an kai ɗauki bayan samun kiran gaggawa guda takwas."
Kannywood ta yi babban rashi
A wani rahoton na daban Allah ya yi wa shahararren darakta a masana'antar shirya fina-finan Hausa, Aminu S Bono, rasuwa ranar Litinin.
Shugaban hukumar tace fina-finai ta jihar Kano, Abba El-Mustapha, ya tabbatar da rasuwar daraktan a shafinsa na soshiyal midiya
Asali: Legit.ng