Zaben Gwamnan Kogi Na 2023: Dino Melaye Ya Nemi a Soke Zabe a Kananan Hukumomi 5

Zaben Gwamnan Kogi Na 2023: Dino Melaye Ya Nemi a Soke Zabe a Kananan Hukumomi 5

  • Sanata Dino Melaye, dan takarar gwamnan PDP a zaben jihar Kogi ya koka kan yadda aka gudanar da zabe a yankin Kogi ta tsakiya
  • Dino ya bukaci hukumar zabe da ta soke zabe a kananan hukumomi biyar na yankin
  • A cewar tsohon dan majalisar, an tafka magudi a kananan hukumomin Okene, Okehi, Ajaoukuta, Adavi, da Ogori/Mangogo

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Jihar Kogi - Dan takarar gwamnan jam'iyyar PDP a jihar Kogi, Sanata Dino Melaye, ya yi kira ga hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) da ta soke zabe a kananan hukumomi biyar na jihar.

Melaye ya ce zaben da aka gudanar a wadannan yankuna na cike da magudi na fitar hankali.

Kara karanta wannan

Labari Da Dumi: Hukumar INEC ta sanar da duka wuraren da aka soke zabe a Kogi

Dino Melaye ya nemi a soke zabe a kananan hukumomi biyar
Zaben Gwamnan Kogi Na 2023: Dino Melaye Ya Nemi a Soke Zabe a Kananan Hukumomi 5 Hoto: @_dinomelaye
Asali: Twitter

Tsohon dan majalisar tarayyar ya lissafa kananan hukumomin da yake son a soke zabe a matsayin Okene, Okehi, Ajaoukuta, Adavi, da Ogori/Mangogo – gaba dayansu a yankin Kogi ta tsakiya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya yi kiran ne a shafinsa na dandalin X (wanda aka fi sani da Twitter a baya) @_dinomelaye

"Ya zama dole INEC ta soke zabe a kananan hukumomi 5 na Kogi ta tsakiya. Zaben da aka yi a Okene, Okehi, Ajaoukuta, Adavi, da Ogori/Mangogo duk suna cike da zamba na fitar hankali."

Dino Melaye ya lashe rumfarsa

A wani labarin, mun ji cewa Sanata Dino Melaye, ɗan takarar gwamnan jihar Kogi a inuwar jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ya samu nasarar lashe rumfar zaɓen da yake kaɗa kuri'a.

Tsohon mamban majalisar dattawan ya lallasa jam'iyyar APC da gagarumin rinjaye a rumfar zaɓensa da ke Iluafon quarters, RA: Aiyetoro 1, ƙaramar hukumar Ijumu a jihar Kogi.

Sanata Melaye ya samu ƙuri'u 210 a zaben da aka kaɗa yau Asabar a rumfar zaɓen inda ya lalllasa babban abokin adawarsa na jam'iyyar APC, Usman Ododo, wanda ya samu kuri'u 22.

Asali: Legit.ng

Online view pixel