Yanzu: Shugaba Tinubu Ya Amince da Sabbin Nade-Nade 20, Jerin Sunaye

Yanzu: Shugaba Tinubu Ya Amince da Sabbin Nade-Nade 20, Jerin Sunaye

  • Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin sabbin kwamishinoni 20 domin aiki a hukumar kidaya ta kasa (NPC)
  • Mai ba shi shawara ta musamman kan harkokin labarai, Ajuri Ngelale, ya bayyana cewa mutanen za su yi aiki a matsayin kwamishinonin tarayya
  • Daga cikin kwamishinonin da aka nada akwai guda tara da za su dawo a wa'adi na biyu

Abuja - Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin sabbin kwamishinoni 20 domin su yi aiki a hukumar kidaya ta kasa wato NPC.

Tinubu ya yi sabbin nade-naden ne a cikin wata sanarwa dauke da sa hannun mai ba shi shawara ta musamman kan harkokin labarai, Ajuri Ngelale, a ranar Laraba, 8 ga watan Nuwamba.

Tinubu ya nada sabbin kwamishinonin NPC
Yanzu: Shugaba Tinubu Ya Amince da Sabbin Nade-Nade 20, Jerin Sunaye Hoto: @officialABAT
Asali: Twitter

Shugaban kasar ya bukaci sabbin kwamishinonin da masu dawowa da su yi nasarar aiwatar da dukkan matakan da gwamnatinsa ta dauka don samar da ainahin bayanan jama'a.

Kara karanta wannan

Kogi: "Ni ake nema a kashe" Ɗan takarar Gwamna ya tona shirin Gwamnan APC a jihar arewa

A cewarsa, da wadannan bayanai ne za a samar da mafita mai dorewa ga matsalolin tattalin arziki da zamantakewa a kasar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tun bayan rantsar da shi a watan Mayu, shugaban kasar ya yi nade-nade da dama domin tabbatar da ganin ya cimma muradinsa na sabonta fatan yan Najeriya kamar yadda ya yi alkawari.

Jerin sunayen sabbin kwamishinonin NPC

  1. Hon. Emmanuel Trump Eke — Abia
  2. Dr. Clifford Zirra — Adamawa - An sake nada shi ne
  3. Mista Chidi Christopher Ezeoke — Anambra - An sake nada shi ne
  4. Barr. Isa Audu Buratai — Borno - An sake nada shi ne
  5. Bishop Alex Ukam — Cross River
  6. Ms. Blessyn Brume-Ataguba — Delta
  7. Dr. Jeremiah Ogbonna Nwankwegu — Ebonyi
  8. Dr. Tony Aiyejina — Edo - An sake nada shi ne
  9. Mista Ejike Ezeh — Enugu - An sake nada shi ne
  10. Mista Abubakar Damburam — Gombe - An sake nada shi ne
  11. Farfesa Uba Nnabue — Imo - An sake nada shi ne
  12. Ms. Sa'adatu Dogon Bauchi Garba — Kaduna
  13. Dr. Aminu Ibrahim Tsanyawa — Kano
  14. Hon. Yori Afolabi — Kogi
  15. Hon. Olakunle Sobukola — Ogun
  16. Hon. Temitayo Oluseye Oluwatuyi — Ondo
  17. Sen. Mudashiru Hussain — Osun - An sake nada shi ne
  18. Ms. Mary Ishaya Afan — Plateau
  19. Mista Ogiri Itotenaan Henry — Rivers
  20. Mista Saany Sale — Taraba - An sake nada shi ne

Kara karanta wannan

Kano: Hisbah ta yi martani kan aske kan wata budurwa da kwalba, ta fadi matakin da ta dauka a kai

Tinubu ya rattaba hannu a kasafin kudi

A wani labarin, mun kawo a baya cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu a kan karin naira tiriliyan 2.17 na kasafin kudin 2023.

Kamar yadda jaridar The Cable ta rahoto, Tinubu ya sanya hannun ne a ranar Laraba, 8 ga watan Nuwamba, a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Asali: Legit.ng

Online view pixel