Fitaccen Malamin Addini Ya Bayyana Mafita 1 Tak Ga Matsalolin Najeriya

Fitaccen Malamin Addini Ya Bayyana Mafita 1 Tak Ga Matsalolin Najeriya

  • Fitaccen malamin addini, Bishop Matthew Kukah, ya magantu a kan matsalolin da suka addabi Najeriya
  • Limamin cocin na Katolika ya ce duk wani dan Najeriya yana sane da matsalolin da kasar take fuskanta a halin da ake ciki
  • Sai dai kuma, ya ce sai yan Najeriya da shugabanni masu kishin kasa sun hadu ne za a iya magance lamarin

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

Jihar Bayelsa - Limamin cocin katolika na Sokoto, Bishop Matthew Kukah, ya ayyana cewar matsalolin Najeriya abu ne da za a iya shawo kansu.

Ya bayyana cewa duk dan Najeriya ya san matsalolin da kasar ke fuskanta a yanzu haka kuma mutane ne za su yi azamar magance matsalolin, rahoton Vanguard.

Kara karanta wannan

Ministan Tinubu da hatsarin jirgin sama ya rutsa da shi ya magantu, ya faɗi halin da yake ciki

Bishop Kukah ya ce wadanda suka haddasa matsalolin Najeriya basu tsira ba suma
Fitaccen Malamin Addini Ya Bayyana Mafita 1 Tak Ga Matsalolin Najeriya Hoto: Vanguard
Asali: UGC

Wadanda suka jefa Najeriya a halin da take ciki basu tsira ba - Bishop Kukah

Kukah wanda ya yi jawabi a wajen wani taro da aka gudanar a Yenagoa, jihar Bayelsa a ranar Juma'a, 3 ga watan Nuwamba, ya bayyana cewa hatta ga wadanda suke da alhakin jefa Najeriya cikin matsaloli basu tsira ba.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Malamin addinin wanda ya bayyana cewa ya samu damar haduwa da gaba daya shugabannin kasa da na mulkin soja a Najeriya baya ga Janar Sani Abacha, ya ce dukkaninsu suna da niyar bunkasa kasar amma sun gaza saboda rashin kudirin aiwatar da manufofinsu.

Hanya daya da za a warware matsalolin Najeriya

A cewarsa, kowace kasa a duniya tana da nata matsalolin kuma yan kasa da shugabanni masu kishi ne suke haduwa don magance irin wadannan matsaloli.

Ya bukaci yan Najeriya da su gano ainahin nasu gaskiyar domin samun ci gaba da kyau kamar yadda sauran kasashe suka yi.

Kara karanta wannan

Wani dan Najeriya ya gano yaransa 4 ba nashi bane bayan gwajin DNA, ya koka a bidiyo mai tsuma rai

Jaridar Daily Trust ta nakalto shi yana cewa:

"Abu mai kyau game da Najeriya shine cewa kowa ya san menene matsalolin da ke addabar kasar kuma mutane da ke da alhakin haddasa wadanan matsalolin suma basu tsira ba, suma basu san menene zaman lafiya ba.
"Yan Najeriya na magana kan sauran kasashe, ina tausayawa yan Najeriya da dama wadanda da kyar suke iya zuwa wuraren da ke makwabtaka da su saboda matsaloli da dama balle a kai ga zuwa sauran yankunan Afrika da sauran yankunan duniya.
"Koda dai, kowace kasa na da nata matsalolin, kalubalen da ke gabanmu a Najeriya shine cewa, me muke so, shin za mu iya samar da damokradiyya da ci gaban kasarmu? Tambaya ce mai wuyar amsa, domin abin da muke kira duniyar wayewa a yau ita ce shigowar shekaru 200 da aka yi Afrika wacce ta taimaka wajen gina wadannan kasashe.
“Don haka mu da kanmu muna tunanin, me ya sa ba mu zama kamar sauran mutane ba, ba mu zama kamar sauran ba ne saboda ya zama dole kowace kasa ta nemo nata gaskiyar don ci gaba. Ba wai ba za mu iya amfani da damokradiyya don ci gaban Najeriya ba, amma akwai wasu muhimman abubuwa da ya zama dole su kasance a kasa kafin mutane su fahimci damokradiyya.

Kara karanta wannan

FG ta yi karin bayani, ta fara bincike yayin da jirgin sama dauke da ministan Tinubu ya yi hatsari

"Har sai Najeriya ta magance matsalarta, za a dunga yi wa damokradiyya kallo kamar na caca."

Amurka ta gargadi yan kasarta a Najeriya

A wani labarin, mun ji cewa Amurka ta yi gagarumin gargadi ga yan kasarta da ke Najeriya, inda ta sanar da su hatsarin da ke tattare da wasu manyan otel-otel a manyan biranen kasar.

An saki wannan gargadi ne a matsayin karin bayani na gaggawa ga yan kasar Amurka a ranar Juma'a, 3 ga Nuwamba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng