"Gobe Jumu'a" Shugaban Majalisar Wakilai Abbas Ya Yi Bayani Kan Ƙarin Ƙasafin Kuɗin.2023

"Gobe Jumu'a" Shugaban Majalisar Wakilai Abbas Ya Yi Bayani Kan Ƙarin Ƙasafin Kuɗin.2023

  • Shugaban majalisar wakilan tarayya ya ce mai yiwuwa shugaba Tinubu ya rattaɓa hannu kan karin kasafin kuɗin 2023
  • Tajudeen Abbas ya bayyana haka ne bayan majalisun tarayya sun amince da karin kasafin ya zam doka bayan tsallake karatu na uku
  • Bola Tinubu ya ce wannan ƙarin kasafin na kunshe da kuɗin tabbatar da tsaron ƙasa, da tallafin talakawa

Ahmad Yusuf, gogaggen Edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Tajudeen Abbas, kakakin majalisar wakilai ta ƙasa, ya ce da yiwuwar shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu kan karin kasafin kudin 2023 ranar Juma’a.

Abbas ya bayyana haka ne ranar Alhamis bayan kudirin ƙarin kasafin kuɗin wanda ya kai N2.17tr ya tsallake karatu na uku a majalisar dattawa da majalisar wakilai.

Kara karanta wannan

Majalisar tarayya ta amince da ƙarin kasafin kuɗin da Tinubu ya tura na 2023, bayanai sun fito

Shugaban Majalisar wakilan tarayya, Tajudeen Abbas.
Shugaba Tinubu Ka Iya Rattaba Hannu Kan Karin Kasafin 2023, In Ji Abbas Hoto: Tajudeen Abbas
Asali: Facebook

A ranar Talatar da ta gabata ne dai karin kasafin ya tsallake karatu na daya da na biyu a majalisar dattawa da ta wakilai, kamar yadda The Cable ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tun da fari dai, Shugaba Bola Tinubu ya bukaci ‘yan majalisar da su gaggauta amincewa da kudirin ƙarin kasafin kuɗin saboda muhimmancinsa.

Kafin amincewa da kasafin a ranar Alhamis, sai da majalisar ta tafi hutu na ɗan loƙacin kafin daga bisani ta gaggauta dawowa aka kaɗa kuri'ar amince wa da shi.

Dalilin da yasa aka yi saurin amincewa da kasafin

Da yake jawabi kan ci gaban, shugaban majalisar ya ce sun yi haka ne saboda shugaban "zai iya" sanya hannu kan kasafin ya zama doka gobe Juma'a.

Abbas ya ce:

“Abin da muka yi tun da farko shi ne tsarin da muka saba na jira har zuwa ranar da za a kaɗa kuri'a da kuma zartar da shi ya zama doka.

Kara karanta wannan

Majalisar wakilai ta ba AGF wa'adin sa'o'i 72 domin bayar da ba'asi kan N100bn na tallafin COVID-19

Tun a ranar Litinkn ɗin farkon wannan makon, majalisar zartarwa karƙashin Bola Ahmed Tinubu ta amince da ƙarin N2.17tr a kasafin kuɗin shekarar 2023, Channels tv ta tattaro.

Gwamnan Imo ya karya shiru kan abinda ya faru

A wani rahoton kuma Gwamna Hope Uzodinma ya yi magana kan tsautsayin da ya faru har shugaban NLC na ƙasa ya sha wahala a jihar Imo.

Jim kaɗan bayan Bola Tinubu ya miƙa masa tutar APC a Villa, gwamnan ya zargi Joe Ajaero da tsoma hannu a siyasar jihar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262