Shugaba Tinubu Ya Aika Sako Majalisa, Ya Buƙaci Ta Amince da Ƙarin Kasafin 2023 da Wani Abu 1

Shugaba Tinubu Ya Aika Sako Majalisa, Ya Buƙaci Ta Amince da Ƙarin Kasafin 2023 da Wani Abu 1

  • Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci majalisar wakilan tarayya ta amince da N2.1tr a mataayin ƙarin kasafin kuɗin shekarar 2023
  • Shugaban ƙasar ya aike da sakon wannan bukata ne a wata wasiƙa da ya miƙa wa majalisar ranar Talata, 31 ga watan Oktoba
  • Ranar Litini, Ministan kasafin kuɗi da tsare-tsaren ƙasa, Atiku Bagudu, ya ce za a yi amfani da ƙarin kasafin a fannin tsaro da sauransu

Ahmad Yusuf, gogaggen Edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rubuta wasiƙa zuwa majalisar wakilan tarayya kan sabon ƙarin kasafin kuɗi na shekarar 2023.

Channels tv ta tattaro cewa a sakon da ya tura, shugaba Tinubu ya buƙaci majalisar wakilan tarayyan ta amince da N2,176,791,286,033 a matsayin ƙarin kasafin 2023.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya ware wa INEC naira biliyan 18 na zabukan gwamnonin jihohi 3

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.
Shugaba Tinubu Ya Aike da Sako Ga Majalisa, Ya Buƙaci Ta Amince da Karin Kasafin 2023 Hoto: Bola Ahmed Tinubu
Asali: Facebook

Ya yi bayanin cewa a za a yi amfani da wannan ƙarin kasafin wajen cike gurbin ƙarin albashin da aka yi wa ma'aikatan tarayya, tsaro da sauransu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugaban ƙasar ya kuma aike da daftarin tsarin rage yawan kashe-kashen kuɗi da dabaru na tsakanin 2024-2026 ga majalisar wakilan tarayya.

FEC ta amince da ƙarin kasafi karo na biyu

Idan baku manta ba a ranar Litinin, 30 ga watan Oktoba, 2023, majalisar zartarwa (FEC) ta amince da N2.1tr a matsayin ƙarin kasafin shekarar 2023.

Da yake jawabi bayan taron FEC a Abuja, Ministan Kasafin Kudi da Tsare Tattalin Arziki, Atiku Bagudu, ya ce an yi ƙarin kasafin kudin ne don magance batutuwan gaggawa.

"Majalisar ta yi duba tare da la'akari da bukatar karin kasafi karo na biyu a shekarar 2023," in ji shi a fadar gwamnati da ke Abuja, The Nation ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya amince da ƙarin Naira tiriliyan 2.18 a kasafin kuɗin 2023, ya faɗi ayyukan da za a yi

"Daga nan aka amince da N2,176,791,286,033 a matsayin karin kasafin kudin, kuma wannan karin kasafin kudin za a yi amfani da shi a harkoki gaggawa da suka hada da Naira biliyan 605 na tsaron kasa."

Ministan ya bayyana cewa ƙarin kasafin ya kunshi kuɗin da za a cike gurbin ƙarin albashin da aka yi wa ma'aikata da kuɗin da FG zata raba wa magidanta don rage radaɗi.

APC ta ƙara rikita PDP

A wani rahoton kuma Jam'iyyar APC ta ƙara yi wa jam'iyyar PDP babban lahani yayin da zaɓen gwamna ke ƙara kusantowa a jihar Kogi.

Tsohon ɗan takarar gwamna a inuwar PDP da magoya bayansa, mambobin jam'iyyu uku sun sauya sheka zuwa APC.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel