Kwamitin Masallacin Abuja Ya Karyata Jita-jitar Cewa Za a Rushe Bangaren Masallacin

Kwamitin Masallacin Abuja Ya Karyata Jita-jitar Cewa Za a Rushe Bangaren Masallacin

  • Kwamitin gudanarwa na babban masallacin Abuja ya fitar da sanarwa kan jita-jitar rushe bangaren masallacin a Abuja
  • An yi ta yada labarin cewa ministan Abuja, Nyesom Wike ya shirya rushe bangaren masallacin don fadada hanya da ta biyo kusa da masallacin
  • A cikin sanarwar, kwamitin ya musanta wannan labari da ake yadawa inda ya bukaci al'ummar Musulmai su yi watsi da shi

FCT, Abuja - Kwamitin babban masallacin Abuja ya bukaci al'ummar Musulmi da su guji bata sunan ministan Abuja, Nyesom Wike.

Limamin masallacin, Dakta Muhammad Kabir Adam da daraktan kudi, Ambasada Haliu Shu'aib su suka bayyana haka yayin ganawa da manema labarai.

Kwamitin Masallacin Abuja Ya Yi Martani Kan Zargin Rushe Bangaren Masallacin
Kwamitin Masallacin Abuja ya yi martani kan zargin rushe masallacin. Hoto: Nyesom Wike, CON, GSSRS, Ayekooto Akindele.
Asali: Facebook

Meye kwamitin masallacin Abuja ya ce kan jita-jitar?

A ganawar wanda Sakataren hukumar FCDA, Injiniya Shehu Hadi ya shirya, sun karyata cewa za a rusa bangaren masallacin, Legit ta tattaro.

Kara karanta wannan

Za Su Kashe Ni – Abokin Fadan Kwankwaso a NNPP Ya Ce Ya Na Fuskantar Barazana

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hukumar wanda Wike ke jagoranta tun farko ta musanta zargin wanda daga bisani kwamitin masallacin ya tabbatar.

Sanarwar ta ce:

"Hukumar masallacin Abuja ta samu labarin da ya ke yawo na shirin rushe bangaren masallacin wanda ke jawo hatsaniya a tsakanin al'ummar Musulmai.
"Ya kamata mutane su yi watsi da wannan labarin kanzon kurege da ake yadawa."

Meye ya jawo kace-nace kan masallacin Abuja?

Wannan na zuwa ne bayan jita-jitar da ake yadawa na shirin rushe bangaren masallacin don fadada hanya, cewar Vanguard.

Al'ummar Musulmai sun yi tir da Allah wadai da wannan kudiri inda su ka zargi ministan Abuja, Wike da nuna tsantsar kiyayya ga addinin Musulunci.

A martaninshi, Wike ya ce ko kadan ba ya gaba da Musulunci inda ya ce babu wanda ya ke martabawa fiye da kowa kamar Sarkin Musulmi, Sultan Sa'ad Abubakar.

Kara karanta wannan

Shetty, El-Rufai da Sauran Mutum 5 da Tinubu Ya Ba Mukamai, Sai Ya Dawo Ya Karbe

Wike: Fasto ya roki Tinubu ya kama Gumi

Kun ji cewa, Fasto Elijah Ayodele ya bukaci Shugaba Tinubu ya kama Sheikh Ahmed Gumi saboda kalamansa kan ministan Abuja, Nyesom Wike.

Faston ya ce Gumi na son tayar da hankali da kawo rarrabuwar kawuna a tsakanin 'yan kasar.

Sheikh Gumi ya ambaci Wike da shaidanin mutum inda ya bukaci Shugaba Tinubu ya sauya shi da Musulmi don dakile shirinsa na rushe Musulunci.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.