Tinubu Ya Nada Shugabanni a Hukumomin NIPOST, NCC, NITDA Da Sauransu

Tinubu Ya Nada Shugabanni a Hukumomin NIPOST, NCC, NITDA Da Sauransu

  • Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da sabbin nade-nade a ma'aikatar sadarwa da kirkire-kirkire da tattalin arzikin zamani
  • Tinubu ya nada sabbin shugabanni a hukumomin NIPOST, NCC, NITDA, NIGCOMSAT da NDPC
  • An kuma sanar da nadin mai ba shugaban kasa shawara ta musamman kan fasaha da tattalin arziki na zamani - Idris Aubankudi

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da nadin shugabanni a Hukumar Sadarwa ta Najeriya (NCC), Hukumar Aika Sakonni ta Najeriya (NIPOST), da Hukumar bunkasa ilimin fasahar sadarwa ta Najeriya (NITDA).

Sauran hukumomin da aka yi sabbin nade-nade sun hada da Hukumar kula da yanayin sararin samaniya ta kasa (NIGCOMSAT) da Hukumar kare bayanan sirrin masu amfani da intanet ta kasa (NDPC).

Shugaban kasa Tinubu ya yi nade-nade masu muhimmanci
Tinubu Ya Nada Shugabanni a Hukumomin NIPOST, NCC, NITDA Da Sauransu Hoto: @officialABAT
Asali: Twitter

Mai ba shugaban kasa shawara ta musamman kan harkokin labarai, Cif Ajuri Ngelale, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya saki a ranar Laraba, 11 ga watan Oktoba.

Kara karanta wannan

Idris Alubankudi Saliu: Abubuwa 10 a Game da Sabon Hadimin Bola Tinubu

Ngelale ya ce sabbin nade-naden da shugaban kasar ya yi suna karkashin karkashin ma'aikatar sadarwa da kirkire-kirkire da tattalin arzikin zamani.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

  • Shugaban Hukumar Sadarwa ta Najeriya (NCC) - Aminu Maida
  • Manajan Darakta/Shugabar Hukumar kula da yanayin sararin samaniya ta kasa (NIGCOMSAT) - Nkechi Egerton-Idehen
  • Darakta Janar/Shugaban Hukumar bunkasa ilimin fasahar sadarwa ta Najeriya (NITDA) - Kashifu Inuwa Abdullahi
  • Kwamishinan kasa/ Shugaban Hukumar kare bayanan sirrin masu amfani da intanet ta kasa (NDPC) - Dr. Vincent Olatunji.
  • Shugaban Hukumar Aika Sakonni ta Najeriya (NIPOST) - Tola Odeyemi

Ya kuma sanar da cewar shugaban kasa Tinubu ya amince da nadin mai ba shugaban kasa shawara ta musamman kan fasaha da tattalin arziki na zamani - Idris Aubankudi.

Ya kuma bayyana cewa sabbin nade-naden sun fara aiki nan take.

Kara karanta wannan

Cikakken Jerin Takardun Karatun da Tinubu, Atiku, Peter Obi, Kwankwaso Suka Ba INEC Kafin Zaben 2023

Shugaba Tinubu ya bukaci majalisa ta amince da sabbin nade-nade 17

A wani labarin, shugaban ƙasa Bola Tinubu ya nemi majalisar wakilai da ta amince da naɗin shugaban da hukumar raya yankin Neja Delta (NDDC) da mambobin hukumar.

A cewar shugaba Tinubu, bukatarsa ​​ta yi daidai da tanadin sashe na 2(2) na dokar hukumar raya yankin Neja Delta, cewar rahoton jaridar The Nation.

Ben Kalu, mataimakin kakakin majalisar wakilai, ya karanta wasikar shugaban ƙasa a zauren majalisar a ranar Talata, 10 ga watan Oktoba, rahoton Vanguard ya tabbatar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng