An Kama Malami da Dillali Kan Zargin Sayar da Filayen Bakin Titi a Abuja

An Kama Malami da Dillali Kan Zargin Sayar da Filayen Bakin Titi a Abuja

  • Jami'an tsaro sun kama Malamin Coci da wani mutum ɗaya bisa zargin damfarar mazauna haramtattun gine-gine a Abuja
  • Rahoto ya nuna waɗan da ake zargin sun fara karɓan kuɗaɗe daga mutanen don kare su daga rusau
  • Kwamishinan 'yan sandan Abuja ya bada umarnin gudanar da bincike mai zurfi gabanin gurfanar da su a Kotu

FCT Abuja - Jami’an tsaro da ke aiki a babban birnin tarayya Abuja sun kama wasu mutane biyu da ake zargi da satar fili, Yusuf Garba Ibrahim wanda ake kira Baba Khalifa da Fasto Emmanuel Ayisa.

Rahoton Daily Trust ya ce an kama mutanen biyu bisa zargin karɓan ƙudaɗe daga wasu mutane a kewayen wasu haramtattun gine-gine da matsugunai a Jahi da Kado.

Yan sanda sun yi kame a Abuja.
An Kama Malami da Dillali Kan Zargin Sayar da Filayen Bakin Titi a Abuja Hoto: Dailytrust
Asali: UGC

An tattaro cewa ana ci gaba da tafka ta’asa ba bisa ka’ida ba a kan titin da ke tsakanin unguwannin Kado da Jahi a birnin Abuja, inda aka dade da jingine aikin titin.

Kara karanta wannan

Kotu Ta Yanke Wa Babban Malami da Ɗan Uwansa Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Abu 1

Tawagar rundunar hadin gwiwa ta Abuja ne suka yi wannan kame jiya biyo bayan samun bayanan sirri da ke nuna mutane na harhaɗa wa waɗan da ake zargi kuɗaɗe.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yadda asirin Fasto da mutumin ya tonu

Sakataren rundunar haɗin guiwa ta FCTA, Peter Olumuji, ya ce jami'an tsaro sun tattara bayanan leƙen asiri cewa masu haramtattun gine-gine da tantuna suna haɗa wa wasu kuɗi.

Bayanan sun nuna cewa mutanen suna haɗa kuɗin ne domin tsira daga shirin risau da ma'aikatar Abuja zata yi.

Nan da nan jami'an tsaro suka zaƙulo ainihin waɗanda ake haɗa wa kuɗin kuma suka garzaya suka cafke su.

Olumuji ya bayyana cewa kwamishinan ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja ya ba da umarnin a gudanar da cikakken bincike kafin a gurfanar da su gaban kuliya.

Ya ce:

"Hukunta su zai zama darasi ga masu damfarar mutane waɗanda shirin rusau zai shafa a Anguwannin, wannan abu ne da FCTA ba zata lamurta ba."

Kara karanta wannan

Gwamnan APC Ya Fara Raba Wa Talakawan Jiharsa Kuɗi N5,000 Duk Wata Don Rage Musu Radaɗi

Primeboy Ya Mika Kansa Ga Yan Sanda Bayan Ayyana Nemansa Ruwa a Jallo

A wani rahoton kuma Primeboy, abokin fitaccen mawaƙin nan da ya mutu Mohbad ya miƙa kansa ga rundunar yan sandan jihar Legas.

Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar 'yan sandan jihar, Benjamin Hundeyin, shi ne ya tabbatar da haka a wata sanarwa da ya wallafa a.shafinsa na manhajar X.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel