Mataimakiyar Sakataren SSANU Ta Kwanta Dama Sanasin Hatsarin Mota

Mataimakiyar Sakataren SSANU Ta Kwanta Dama Sanasin Hatsarin Mota

  • Ƙungiyar manyan ma'aikatan jami'o'in Najeriya ta yi babban rashi sanadin hatsarin mota ranar Alhamis, 28 ga watan Satumba
  • Mataimakiyar babban sakataren SSANU na ƙasa, Esther Ezeama, ta mutu a haɗarin mota yayin da take hanyar zuwa jami'ar Maiduguri
  • Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Kwamared Ibrahim, ya bayyana cewa sun yi babban rashin mace mai kwazo da aiki tuƙuru

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Mataimakiyar babban sakataren kungiyar manyan ma'aikatan jami'o'in Najeriya (SSANU), Esther Ezeama, ta rasu a wani hatsarin mota a ranar Alhamis.

Rahoton Daily Trust ya ce wani mummunar hatsari ya rutsa da ita a hanyar zuwa taron majalisar zartarwa na SSANU karo na 45 da aka gudanar jiya a jami’ar Maiduguri.

Kungiyar SSANU ta yi babban rashi.
Mataimakiyar Sakataren SSANU Ta Kwanta Dama Sanasin Hatsarin Mota Hoto: vanguardngr
Asali: UGC

Shugaban ƙungiyar manyan ma'aikatan jami'o'in na ƙasa, Kwamared Mohammed Haruna Ibrahim, shi ya tabbatar da rasuwar Esther ga 'yan jarida.

Kara karanta wannan

Jami'an Tsaro Zasu Kama Kwankwaso Kan Barazana Ga Rayuwar Alkalan Kotu? Sabbin Bayanai Sun Fito

Ya ce Esther ta rasa ranta ne a wata mota da ta ɗebo ma’aikatan sakatariyar SSANU ta kasa a wani wuri mai nisan kilomita 24 zuwa garin Bauchi a jihar Bauchi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mun yi babban rashi - SSANU

Ibrahim ya kuma bayyana cewa rasuwarta babban rashi ne ga kungiyar SSANU da kuma iyalan da ta rasu ta bari.

Shugaban ƙungiyar ya ƙara da bayanin cewa marigayiyar tana da kyawawan ɗabi'u, inda ya bayyana ta a matsayin mai tawali’u, mutuntaka, mai kwazo da uwa uba aiki tukuru.

A kalamansa ya ce:

"Kwanan nan ta aje aiki a jami'ar tarayya da ke Jos (babban birnin jihar Filato) inda ta kai matsayin Darakta kafin ta yi ritaya."
"Kuma ita mace ce da ta iya magana da harsunan ƙasashen waje kusan guda uku ban da yaren Hausa, Yarbanci da Igbo wanda ta iya a nan cikin gida."

Kara karanta wannan

Gwamnan Arewa Ya Bada Hutun Ranar Haihuwar Manzon Allah SAW Bayan Wanda Gwamnatin Tinubu Ta Sanar

Daga ƙarshe ya yi addu'ar Allah ya bai wa iyalanta haƙurin jure wannan rashi na farat ɗaya da suka yi ba zato ba tsammani, kamar yadda Naija News ta ruwaito.

Barazana Ga Alkalai: Da Gaske Za a Kama Kwankwaso? Sabbin Bayanai Sun Fito

A a wani rahoton na daban Wata ƙungiyar yaƙi da ta'addanci a Najeriya ta yi kira da a kama Sanata Kwankwaso bisa zargin yi wa alƙalai barazana.

Shugaban NCAT na ƙasa, Kwamared Terrence Kuanum, ya yi gargadin cewa akwai bukatar a dakile wuce gona da iri da 'yan Kwankwasiyya ke yi ba tare an taka musu birki ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262