Gwamnatin Abba Gida Gida Na Shirin Rusa Gadar Gwarzo? Gaskiya Ta Bayyana

Gwamnatin Abba Gida Gida Na Shirin Rusa Gadar Gwarzo? Gaskiya Ta Bayyana

  • Gwamnatin Abba Gida Gida ta yi watsi da rade-radin cewa tana shirin rusa gadar Gwarzo da ke jihar Kano
  • Kwamishinan labarai na jihar, Malam Halilu Dantiye, ya ce gwamnatin Kano ta tura tawagar injiniyoyi domin su duba gadar don aiki a kanta
  • Al'ummar yankin Gwarzo dai sun gudanar da zanga-zanga bayan samun labarin cewa gwamnati na shirin rusa gadar da Sanata Jibrin ya sake ginawa

Jihar Kano - Gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa bata shirin rusa wata gada a garin Gwarzo, hedkwatar karamar hukumar Gwarzo.

An tattaro cewa mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin ne ya gina gadar.

Gwamnatin Kano ta ce bata shirin rusa gadar Gwarzo
Gwamnatin Abba Gida Gida Na Shirin Rusa Gadar Gwarzo? Gaskiya Ta Bayyana Hoto: @Kyusufabba
Asali: Twitter

Gwamnatin Abba gida gida ta tura injiniyoyi don su duba aikin gadar Gwarzo

Kwamishinan labarai da harkokin cikin gida na jihar Kano, Malam Halilu Dantiye ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a garin Kano a ranar Laraba, 6 ga watan Satumba, Daily Trust ta rahoto.

Kara karanta wannan

Ahaf: Uba Sani ya kama lagon PDP, ya ce shaidun adawa sun nuna shi ya ci zabe

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Ya ce wasu mutane sun tunkari gwamnatin jihar karkashin jagorancin Abba Kabir Yusuf wanda aka fi sani da Abba Gida Gida suna masu neman a sake gina gadar wacce ta rushe.

A cewarsa, tuni gwamnati ta tattara tawagar injiniyoyinta da suka duba gadar da abin ya shafa, ya kara da cewa ana ci gaba da gudanar da aikin da ya kamata a gadar.

Dantiye ya kuma ce gwamnatin na jiran samun rahotannin gina gadar ta hanyar da ta dace.

Al'ummar Gwarzo sun fusata kan rade-radin rusa gadar yankin

Tun farko dai, jaridar The Guardian ta rahoto cewa hankula sun tashi a karamar hukumar Gwarzo ta jihar Kano bayan rade-radin cewa gwamnati na shirin rusa gadar da Sanata Barau ya sake ginawa.

Hakan ya fusata al'umma inda mazauna garin Gwarzo da ke yankin Kano ta arewa suna gudanar da zanga-zanga don nuna rashin amincewarsu kan wannan yunkuri da gwamnatin ke yi.

Kara karanta wannan

An sake shiga matsi: Ta'azzarar barnar 'yan bindiga ta sa an rufe kasuwannin shanu 8 a Arewa

An tattaro cewa gadar ta rushe ne kimanin mako uku da suka gabata sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi a yankin.

Biyo bayan tsaiko da aka samu a wajen zirga-zirgar ababen hawa, mazauna yankin sun nemi gwamnatin jihar ta sa baki domin gyara ta, amma abin ya ci tura.

Amma daga karshe sai aka sami taimako a lokacin da Sanata Jibrin ya umarci wani dan kwangila ya gyara gadar.

Ba a bi tsari wajen sake gina gadar ba, Kwamishinan ayyuka na jihar Kano

Sai dai kuma, kwamishinan ayyuka na jihar, Marwan Ahmad, ya bayyana cewa ba a bi tsarin da ya kamata ba wajen sake gina gadar.

Ya soki tsoma bakin da Jibrin ya yi a lokacin da gwamnati ke kammala shirye-shiryen sake gina gadar.

A cewar kwamishinan, Sanata Jibrin (Kano ta Arewa) bai nemi izini da amincewar gwamnatin jihar ba kafin ya fara aikin.

Ya dage cewa Sanatan ba shi da hurumin gudanar da aikin gina hanyar gwamnatin jihar.

Kara karanta wannan

Kitimurmura yayin da gwamnatin jiha ta garkame fitaccen gidan rediyo da TV

Nadin Mukamai: Abba Gida Gida Ya Jawo Matasa 44, Ya Sakala a Ma’aikatun Kano

A wani labarin, mun ji cewa Abba Kabir Yusuf ya dauko matasa ya ba su wani mukami da aka kira SSR da SR watau masu tattara rahotanni na musamman daga MDAs.

Malam Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar da sanarwa a shafinsa a matsayinsa na babban sakataren yada labaran Mai girma gwamnan Kano.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng

Online view pixel