Gwamnatin Najeriya Ta Magantu Kan Juyin Mulki Yayin Da Sojoji Suka Hambarar Da Gwamnati a Gabon Da Nijar

Gwamnatin Najeriya Ta Magantu Kan Juyin Mulki Yayin Da Sojoji Suka Hambarar Da Gwamnati a Gabon Da Nijar

  • Yayin da ake ci gaba da samun karuwar juyin mulki a nahiyar Afirka, gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi watsi da duk wata fargaba na juyin mulki
  • A cewar gwamnatin tarayya, kasar ta wuci zamanin hambarar da gwamnati ta karfin tuwo
  • Mohammed Idris Malagi, ministan labarai da wayar da kan yan kasa ya ce, Najeriya ta kasance kasar damokradiyya tsawon wannan lokaci inda cibiyoyin damokradiyya ke kara karfi

Abuja - Mohammed Idris, ministan labarai da wayar da kan yan kasa, ya yi watsi da fargabar da ake yi na kar sojoji su yi juyin mulki a Najeriya.

Idris ya ce kasar ta wuce wannan matakin da dadewa.

Gwamnatin tarayya ta ce Najeriya ta wuci juyin mulkin sojoji
Gwamnatin Najeriya Ta Yi Jawabi Game Da Fargabar Juyin Mulki Yayin da Sojoji Suka Kwace Mulki a Gabon da Nijar Hoto: @FMINONigeria, @officialABAT
Asali: Twitter

Juyin mulki: "Mun wuci wannan", minista

Ministan ya bayyana cewa cibiyoyin damokradiyya na da karfi sosai a Najeriya, don haka ba zai zama abu mai sauki ga manyan jami'an sojoji su hambarar da zababbun shugabannin damokradiyya ba.

Kara karanta wannan

"Mu Makota Ne" Shugaba Tinubu Ya Bude Gaskiya Kan Yaki da Sojojin Jamhuriyar Nijar

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

An bayyana matsayin gwamnatin tarayya ne a cikin wani rahoto da jaridar Punch ta fitar a ranar Asabar, 2 ga watan Agusta.

Ministan ya ce:

"Zan iya fara maku babu tsoro ko fargaba ko kadan. Mun wuci wannan, kuma mun kasance kasar damokradiyya tsawon wannan lokaci tare da cibiyoyin damokradiyya da ke kara karfi."

Juyin mulki: Fargabar da nake ta tabbata, Tinubu

A baya Legit.ng ta rahoto cewa Shugaban kasa Bola Tinubu ya bayyana cewa tsoron da ya dunga ji game da juyin mulkin sojoji a Jamhuriyar Nijar ya tabbata da abun da ya faru a Gabon inda sojoji suka tsige Shugaba Ali Bongo ta hanyar kifar da gwamnatinsa.

Shugaban kasar ya ce ya yi fargabar cewa matakin da sojojin juyin mulki a Jamhuriyar Nijar suka dauka zai kafa mummunan tarihi ga nahiyar bakar fata. Fadar shugaban kasa ta bayyana haka a cikin wata wallafa a manhajar X.

Kara karanta wannan

Juyin Mulkin Gabon: Atiku Ya Bayyana Yadda Za Kawo Karshen Kwace Mulki Da Sojoji Ke Yi a Afrika

"Na ji dadin juyin mulkin Gabon" - Fayose

A wani labarin, mun ji cewa tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayodele Fayose, ya nuna jin dadinsa dangane da juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar Gabon da ke Afrika ta tsakiya.

Fayose ya yi martani a kan hambarar da gwamnatin farar hula da sojojin suka yi a kasar Gabon a ranar Juma'a, 1 ga watan Satumba, rahoton Punch.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng