Babu Najeriya Ciki: Seychelles Ce Kan Gaba a Jerin Kasashe 10 Mafi Arzikin 'Yan Kasa a Afirka a 2023

Babu Najeriya Ciki: Seychelles Ce Kan Gaba a Jerin Kasashe 10 Mafi Arzikin 'Yan Kasa a Afirka a 2023

  • Bankin duniya ya fitar da jerin kasashen Afrika 10 mafi arziƙi ta la'akari da abinda mutum ɗaya ke iya samu
  • Masana tattalin arziƙi na kasafta tarin dukiyar ƙasa da yawan mutanen cikinta domin gane yanayin ci gabanta
  • Duk da kasancewar Najeriya mafi tarin dukiya a Afrika, ba ta samu shiga cikin jerin ƙasashen da mutanenta suka fi arziki ba

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Nahiyar Afrika mai ɗauke da ƙasashe 54, ta kasance ita ce ke da kashi 25% na yawan al'ummar duniya.

Afrika na da masu kuɗi da ke tasowa waɗanda daga cikinsu akwai waɗanda ake gogayya da su a duniya.

Duk da yawan jama'a da suka kai aƙalla biliyan 1.2 da kuma tarin albarkatun ƙasa da nahiyar ke da su, babu jin daɗin rayuwa kamar yadda 'yan wasu nahiyoyin ke ji.

Kara karanta wannan

Yanzu-Yanzu: ECOWAS Ta Sake Sanya Sabbin Takunkunmi Kan Juyin Mulkin Jamhuriyar Nijar, Bayanai Sun Fito

Kasashen Afrika 10 mafi arziki
Jerin ƙasashen Afrika 10 mafi arziƙi na 'yan ƙasa. Hoto: Photo Alliance
Asali: Getty Images

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Matakin da aka bi wajen zakulo ƙasashen Afrika 10 mafi arziƙi

A cikin wani rahoto da bankin duniya ya haɗa, an bayyana cewa ƙasar Seychelles, wacce ke da yawan jama'a da aka ƙiyasta su a 100,600, ita ce ta fi kowace ƙasa a Afrika arziki a shekarar 2023.

An yi duba ya zuwa 'GDP Per Capita', ma'ana an raba tarin dukiyar da ƙasa ke da ita da yawan al'ummar da take da su, wanda hakan zai ba da kason da kowa zai iya samu.

Kasar Mauritius ce ke takewa Seychelles baya, yayin da ƙasar Libya ta zo ta uku duk kuwa da irin ƙalubalen da take fuskanta.

Rahoton ya tattaro cewa ƙasar Madagascar, Nijar da Burundi ne ke can ƙasa a jerin ƙasashen na Afrika mafi arziƙi.

Duk da yawan kuɗaɗen da Najeriya ke samu, wanda ya zarce na kowace ƙasa a Afrika kamar yadda yake a Statista, ita ce ta 25 a cikin jerin ƙasashen Afrika mafi arziƙi.

Kara karanta wannan

Sarkin Zazzau Ya Bukaci Iyaye Su Tura Yara Mata Koyon Aikin Likitanci, Ya Ba Da Dalili

Ƙasashen Afrika 10 da suka fi arziƙi a duk mutum 1

ƘasasheKiyasin arziƙin mutum
Seychelles$35,227
Mauritius$26,905
Libya$26,905
Botswana$18,323
Equatorial Guinea$17,396
Afrika ta Kudu$15,904
Algeria$13,209
Tunisia$12,489
Namibia$11,205
Eswatini$10,782

Kuɗaɗen kasashe 10 mafi rauni a Afrika

Legit.ng a baya ta yi rahoto kan kuɗaɗen ƙasashe 10 mafi rauni a Afrika yayin da kowace ƙasa ke fafutukar ganin ta ɗaga darajar kuɗaɗenta.

Kuɗaɗen Najeriya, wato naira, ba su cikin kuɗaɗe mafiya rauni a nahiyar ta Afrika.

Asali: Legit.ng

Authors:
Deen Dabai avatar

Deen Dabai Zaharaddeen Hamisu marubuci kuma ma'aikacin jarida ne da ke da gogewa wajen iya tantance sahihan labarai da na karya. Ya yi digirinsa a jami'ar Ahmadu Bello dake Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Baya ga haka, ya shafe sama da shekaru 5 a bangaren aikin watsa labarai wanda hakan ya bashi gogewa ta musamman a aikin jarida. Za a iya tuntubarsa ta adireshinsa na yanar gizo: deen.dabai@corp.legit.ng