Dukiyar Dangote Ta Ragu da Dala Miliyan 400, Ya Sauka Zuwa Lamba Na 2 a Jerin Attajiran Forbes Africa

Dukiyar Dangote Ta Ragu da Dala Miliyan 400, Ya Sauka Zuwa Lamba Na 2 a Jerin Attajiran Forbes Africa

  • A cikin sa'o'i 24, Dangote ya yi asarar dala miliyan 400, wanda ya sa ya nesanci matsayin Johann Rupert a jerin attajirai
  • Raguwar darajar dukiyar Dangote dai ta faru ne bisa nasaba da faduwar darajar Naira idan aka kwantanta da dala
  • Duk da haka, Dangote ya ci gaba da zama na daya a jerin attajiran Bloomberg, inda aka ce yana da kudin da ya kai dala biliyan 17

Aliko Dangote dai ya sake samun koma baya a yawan kudinsa sakamakon faduwar darajar Naira, lamarin da ya rage darajar kadarorinsa da dukiyarsa na koma kasa da dala biliyan 11.

Arzikin attajirin na Najeriya ya ragu daga dala biliyan 11.2 a ranar 4 ga watan Agusta zuwa dala biliyan 10.8, ya samu faduwar dala miliyan 400 kenan a rana daya kacal a cewar Forbes.

Kara karanta wannan

Karen Mota Ya Yi Karambani da Tirelar Dangote, Ya Ɓurma Gida Ya Murƙushe Yara

Dangote ya samu karayar arziki
Yadda Dangote ya samu karayar arziki a kwanan nan | Hoto: bloomberg.com
Asali: Getty Images

A halin yanzu, a cikin jerin attajirai da aka sabunta a ranar 5 ga Agusta, 2023, Dangote ya koma matsayinsa na daya, inda dukiyarsa ta haura dala biliyan 13.5 ya zuwa lokacin hada wannan rahoton.

Ya aka yi darajar kudinsa ta ragu?

Wannan dai ya biyo bayan rahoton da Legit.ng ta samu a baya cewa attajirin da ya fi kowa kudi a Najeriya ya sauka a matsayin wanda ya fi kowa kudi a Afirka, mukamin da ya kwashe sama da shekaru goma a kai.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

A baya dai dukiyar Dangote ta karu zuwa dala biliyan 11.2, wanda hakan ya sa ya samu damar kwato kambun attajirin da ya fi kowa kudi a Afirka.

Duk da haka, raguwar dukiyarsa a baya-bayan nan ta mayar da shi bayan Johann Rupert, wanda a halin yanzu ke rike da kambun na Dangote a baya da dukiyarsa da ta kai dala biliyan 11.2.

Kara karanta wannan

'Yan Daba Sun Afka Wa Manyan APC, Sun Barnata Kayayyaki Na Miliyoyi, Bayanai Sun Fito

Matsayin Dangote a Forbes da Bloomberg

Kasancewar galibin kadarorin Dangote na Naira ne, ana iya danganta raguwar darajar dukiyarsa da karyewar darajar Naira.

Da arzikin da ya kai dala biliyan 10.8, Forbes ta saka Aliko Dangote a matsayin mutum na biyu mafi arziki a nahiyar Afrika; a Bloomberg kuma yana kan matsayin na daya da adadin kudi sama da dala biliyan 17.

Kamfanoni 10 da Damgote ya mallaka

A bangare guda, Aliko Dangote, dan Najeriyan da ya fi kowa kudi a Afrika kuma mamallakin Dangote Group fitacce ne wajen gina kasuwanci da fafutukar hada-hada a fannoni da yawa.

Bloomberg ta ruwaito cewa, rukunin kamfanin Dangote na harkalla ne ta sukari, siminti da kuma wani fannin da ake kira Nascon Allied Industries.

Wadannan kamfanonin sun kafu da kafafunsu a matsayin na gaba-gaba wajen samar da siminti, sukari da kayayyakin abinci a Najeriya da ma bangarori da yawa a nahiyar Afrika.

Kara karanta wannan

Tirkashi: An Cafke Wani Fasinjan Jirgin Sama Saboda Laifin Satar Naira Miliyan 1

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.