Yan Sanda Sun Bayyana Gaskiyar Yadda Wata Budurwa Ta Mutu a Otal a Anambra

Yan Sanda Sun Bayyana Gaskiyar Yadda Wata Budurwa Ta Mutu a Otal a Anambra

  • Rundunar 'yan sanda reshen jihar Anambra ta bayyana ainihin abinda ya yi ajalin wata budurwa a Otal ɗin Cosmila
  • Jami'in hulɗa da jama'a na rundunar, Tochukwu Ikenga, ya ce budurwar nutsewa ta yi ba duka ne ya yi ajalinta ba
  • Da farko, an yaɗa labarin cewa mamaciyar ta kwashi kuɗi a wurin shagalin Bazday, matasa suka mata dukan kawo wuƙa har ta mutu

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Anambra state - Rundunar ‘yan sanda a jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Najeriya, ta yi magana game da wata mata da aka tsinci gawar ta a wani wurin wanka a Otal din Cosmila da ke Awka, babban birnin jihar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, Tochukwu Ikenga, a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, ya ce rahoton binciken gawar da aka gudanar ya nuna cewa nutsewa ta yi a ruwa.

Kara karanta wannan

Anya Ganduje Zai Kai Labari? Gaskiya Ta Bayyana Kan Wanda Zai Zama Sabon Shugaban APC

Chinyere Awuda.
Yan Sanda Sun Bayyana Gaskiyar Yadda Wata Budurwa Ta Mutu a Otal a Anambra Hoto: premiumtimes.com
Asali: UGC

Ya ce labarin da ake yaɗa wa cewa dukanta aka yi har ta mutu ba gaskiya bane, binciken likitoci ya nuna cewa nutsewa ta yi a ruwa har rai ya yi halinsa, kamar yadda Premium Times ta rahoto.

DSP Ikenga ya ce:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Saɓanin ikirarin da wasu suka yi cewa an yi wa budurwar dukan tsiya har ta mutu, likita ya gano babu alamun rauni a gawar matar."

Kakakin ‘yan sandan ya ce binciken ya yi daidai da rahoton farko na cewa budurwan ta gudu ne kan zargin sata a wurin taron, kuma ba a same ta ba bayan haka.

"Da alama ta fada cikin tafkin ruwan da ba a amfani da shi kuma ta nutse," in ji shi.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mista Adeoye, ya umarci a mika takardar karar zuwa Ofishin Antoni Janar domin tantancewa da kuma ba da shawarwaarin shari’a.

Kara karanta wannan

'Yan Bindiga Sun Harbe Babban Sanata Mai Fada a Ji? Hadimin Gwamna Ya Bayyana Gaskiyar Zance

Asalin labarin farko da ya yaɗu

Matar mai suna Chinyere Awuda, ‘yar shekara 27, an tsinci gawar ta ne a ranar 17 ga watan Yuli, a cikin wurin ninkaya na Otal, kamar yadda jaridar Punch ta rahoto.

Misis Awuda, ‘yar asalin garin Nnobi a karamar hukumar Idemili ta kudu a Anambra, an zarge ta da ɗibar wasu kudade da ake watsawa mai bikin zagayowar ranar haihuwa a cin Otal ɗin.

An ce masu watsa kuɗin suka kamata kana suka yi mata duka har ta mutu, daga bisani kuma suka jefar da gawarta a wurin wanka. Lamarin da shugabannin wurin suka musanta.

DSS Ta Yi Rashin Nasara Kan Dakataccen Gwamnan CBN, Kotu Ta Yanke Hukunci

A wani labarin na daban Babbar Ƙotun Abuja mai zama a Maitama ta yi fatali da buƙatar hukumar DSS na ci gaba da tsare dakataccen gwamnan CBN.

A zaman ranar Alhamis, 27 ga watan Yuli, Alkalin Kotun ya yanke cewa babbar Kotu ba ta da hurumin sauraron bukatar.

Kara karanta wannan

Assha: Wata Amarya Ta Datse Mazaƙutar Angonta Kan Abu 1 a Jihar Katsina

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262

Online view pixel