Kotu Ta Bada Belin Dakataccen Gwamnan CBN, Godwin Emefiele

Kotu Ta Bada Belin Dakataccen Gwamnan CBN, Godwin Emefiele

  • Babbar kotun tarayya mai zama a Ikoyi, jihar Legas ta bada belin dakataccen gwamnan CBN, Godwin Emefiele kan kuɗi N20m
  • Alkalin Kotun mai shari'a Nicolas Oweibo ya gindaya sharuɗɗa masu tsauri kafin sakin Emefiele a matsayin beli
  • A ɗazu ne jami'an DSS suka gurfanar da tsohon gwamnan CBN a gaban Kotu bisa zargin mallakar makamai ba kan doka ba

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Lagos State - Ƙotu ta bayar da belin tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), Mista Godwin Emefiele, kan kudi naira miliyan 20.

Sharuɗɗan da Kotun ta gindaya na belin sun haɗa da gabatar da wanda zai tsaya masa, wanda ya mallaki kadarori a kewayen inda Kotu ke zama a Ikoyi, jihar Legas.

Dakataccen gwamnan CBN a Kotu.
Kotu Ta Bada Belin Dakataccen Gwamnan CBN, Godwin Emefiele Hoto: @thecable
Asali: Twitter

Haka zalila shi kansa, Emefiele, zai miƙa Fasfonsa na tafiye-tafiye sannan kuma ya gabatar da ma'aikacin gwamnatin da zai tsaya masa, wanda bai gaza mataki na 16 ba.

Kara karanta wannan

Daga Karshe, Hukumar DSS Ta Gurfanar da Dakataccen Gwamnan CBN a Kotu, Sabbin Bayanai Sun Fito

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa Emefiele ya jima a tsare kafin daga bisani aka gurfanar da shi gaban mai shari'a Nicholas Oweibo na babbar kotun tarayya da ke Legas, ranar Talata.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Wane zarge-zarge gwamnatin tarayya ke wa Emefiele?

Masu shigar da kara suna tuhumar Mista Emefiele da mallakar bindiga ƙirar JOJEFF MAGNUM 8371 ta haramtacciyar hanya watau mara lasisi.

Jami'an hukumar 'yan sandan farin kaya (DSS) ne suka kawo tsohon gwamnan CBN ɗin gaban Kotu cikin tsattsauran tsaro ranar Talata, 25 ga watan Yuli, 2023.

Vanguard ta rahoto cewa Jami'an DSS tare da Emefiele sun isa harabar Kotu da misalin ƙarfe 9:23 na safiyar Talata a cikin motar Hillux fara, wacce aka rufe lambarta.

Daga isarsu Kotun, Mista Emefiele ya fito daga motar tare da taimakon wata mata wacce har kawo yanzu ba a iya tantance bayananta ba.

Kara karanta wannan

Dubu Ta Cika: An Kama Mutane Sama da 100 Kan Zargin Aika Muggan Laifuka Daban-Daban a Arewa

Bayan haka ne kuma aka gurfanar da shi gaban Kotun karkashin mai shari'a Nicolas Oweibo, wanda zai jagoranci shari'ar.

Gwamna Uba Sani Ya Yi Sabbin Nade-Nade Masu Muhimmanci a Kaduna

A wani labarin kuma Gwamna Malam Uba Sani na jihar Kaduna ya yi sabbin naɗe-naɗe masu muhimmanci a gwamnatinsa.

Uba Sani ya bayyana cewa ya yi la'akari da tarihin siyasa, gaskiya da riƙon amana da sadaukarwa wajen gina jihar Kaduna yayin zaƙulo mutanen da ya naɗa muƙaman.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262